A cikin wata sanarwa da Gwamna Uba Sani ya sanya wa hannu, ta yi godiya ga shugaban kasa da jami’an bisa abin da ya ce namijin kokarin da suka yi na ganin an kubutar da daliban ba tare da sun yi ko kwarzane ba.
Gwamnatin Kaduna ta ce ta ceto daliban Kuriga gaba dayansu
ECOWAS ta yi Allah wadai da harin da aka kai wa sojojin Nijar da ya yi sanadiyar rasa rayukan 23 daga cikin su
‘Yan bindiga sun harbi mutane biyu a Mairuwa jihar Katsina ana tsaka da sallar ‘taraweeh’
Wasu mutane dauke da muggan makamai sun kai hari a kauyen Mairuwa na karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina a cikin daren Asabar din nan.
Saukar farashin Dala ya sa wasu kayan abinci sun fara sauka a Nijeriya
Buhari yayi yunkurin rufa wa Nyako asiri kan zargin almundahana
Tsohon Ministan Shari’a na Najeriya Micheal Aondoaka ya baiyana wa kotu cewa tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yayi rufa-rufa kan zargin badaƙala ta Naira biliyan 29 da ake ga tsohon gwamnan jahar Adamawa Murtala Nyako tun bayan saukar sa a mulki a shekarar 2015.
An sake gurfanar da tsohon gwamnan na Adamawa da ɗansa Abdulaziz Nyako Alhamisɗinnan a wata babbar kotu da ke Abuja bisa zargin yin sama da fãdi da Naira biliyan 29, zargin da aka fara shari’a kansa tun ranar 8 ga watan Yulin shekarar 2015.
Tsohon ministan shari’an ya fadawa alkali, mai Shari’a Peter Lifu cewa, tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya umurci tsohon ministan shari’a na lokacin sa Abubakar Malami ya nemi hanyar sasantawa da hukumar EFCC dan ganin a janye wannan ƙãra.
EFCC dai tana tuhumar Nyakon da ɗansa, da kuma wasu guda biyu Zulƙifik Abba da Abubakar Aliyu da wasu Kamfanoni guda uku Blue Opal Ltd, da Tower Assets Management Ltd da kuma Crust Energy Ltd da laifuka 37 da suka hada da zargin sãta, hadin baki da kuma yin karan tsaye ga dokokin aikin ofis.
Ban yarda da zargin da gwamnatin Tinubu ta yi ga waɗannan bayin Allah ba
Shahararren malamin addinin Musulunci a Najeriya Sheikh Ahmad Gumi yana ƙalubalantar gwamnatin Najeriya bisa zargin wasu da aka fitar da jērin sunayen su cewa suna da hannu dumu-dumu a ayyukan ta’addanci a ƙasar.
Gwamnatin Najeriya ta hannun hukumar da ke tattara bayanan sirri kan ilahirin harkokin da suka jībanci kudade a faɗin ƙasar, ta fitar da bayanai dake nuni ga wasu ɗaiɗaikun mutane da kamfanoni har ma da masu harkar canjin kuɗaɗen ƙasashen ƙetare da hannu wurin tallafawa ayyukan ta’addanci, musamman da kuɗaɗe.
Sheikh Ahmad Gumi ya ce jami’an tsaro basu da hurumin aiyana wani a matsayin mai tallafawa taaddanci da kuɗaɗe saboda a cewar sa ‘yan ta’addan su ke ɗaukar nauyin kansu da kansu, ta amfani da kuɗaɗen fansa da suke samu idan suka yi garkuwa da mutane.
Malamin addinin a baya-bayanan ya bukaci gwamnatin Najeriya ta basu damar tattauna wa da yan ta’adda da suka sãce ɗalibai kusan ɗari uku garin Kirga dake jahar Kaduna, saboda da yace da alama abin zai yi matuƙar wahala ga jami’an tsaro, yana mai cewa bai kamata a zuba idanu ana gani shugaba Tinubu ya maimaita irin kurakurai da tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yai ba, na ƙin yin sulhu da ‘yan fashin na dãji.
Tinubu ya haramta wa ministocinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare
Tinubu ya haramta wa ministocinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayar da umurnin haramta wa ministocinsa da sauran mukarraban gwamnatinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen waje.
Shugaba Tinubu ya ba da umurnin ne ta cikin wata wasika da shugaban ma’aikatansa, Femi Gbajabiamila, ya aike wa sakataren gwamnatin tarayya, George Akume.
A cikin wasikar, mai kwanan wata 12 ga Maris, 2024, Tinubu ya ba da umurnin hana duk wasu tafiye-tafiye zuwa kasashen waje.
Sai dai ya ce an keɓance tafiyar da ta zama wajibi.




