Thursday, April 9, 2026
Home Blog Page 452

Katsina za ta karbi bakuncin taron inganta tsaro da zaman lafiya na shiyyar arewa maso yamma

Gwnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da hadin guiwa tsakanin gwamnatin jihar da shirin bunkasa kasashe na majalisar dinkin duniya UNDP su karbi bakuncin taron inganta tsaro da samar da zaman lafiya a shiyyar arewa maso yammacin Nijeriya a jihar Katsina.
Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Barr Abdullahi Garba Faskari ya sanar da hakan a lokacin kaddamar da kwamitin tsare-tsaren yadda za a karbi bakuncin a madadin Gwamnan.
Taken taron shi ne dabarun inganta tsaro da zaman lafiya: shawo kan matsalolin ayyukan ta’addanci da sauyin yanayi.
Kwamitin na kunshe da mambobi 14 da Sakataren Gwamnatin jihar ne shugaba, sannan akwai shugaban ma’aikatan jihar Katsina da kwamishinonin yada labarai da na tsaro da lamurran cikin gida da kuma na shari’a.
A cikin wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ofishin Sakataren Gwamnatin jihar Katsina, Abdullahi Aliyu Yar’adua, ta ce daga cikin nauyin da aka dora wa kwamitin akwai hada hannu da shirin UNDP da sauran hukumomin da suka dace don karbar bakuncin taron yadda ya dace a Katsina.
Kazalika, kwamitin zai shiga ya fita don ganin an saukaka zirga-zirga ga bakin da za su halarci taron, samar da wurin da Taron zai gudana, gayyatar baki da sauran abubuwan da suka shafi wannan taro.

Kullum sau biyu nake magana da shugaba Tinubu kan matsalar tsaro – Uba Sani

 Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya ce a kowace rana yana magana da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu sau biyu yana bayyana masa halin matsalar tsaro da ake fama da ita a jihar. 

 Uba Sani ya bayyana haka ne a wata hira da yayi da gidan talabijin na Channels TV a Siyasar Yau. 

 A ranar 8 ga Maris, ‘yan bindiga sun kai hari a makarantar firamare da karamar sakandare ta LEA, Kuriga sannan suna ci gaba da kai hare-hare a yankunan jihar daban-daban 

Gwamnatin Nijeriya ta roki kungiyoyin SSANU da NASU su janye yajin aikin gargadi

 

Gwamnatin tarayya ta yi kira ga kungiyoyin manyan ma’aikatan jami’o’in kasar, SSANU, daNASU, da su janye yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai da suka fara gudanarwa a ranar Litinin. 

Karamar ministar kwadago da samar da nagartar aiki Nkeiruka ce ta yi wannan roko a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar, Olajide Oshundun a ranar Litinin a Abuja.

Idan dai ba a manta ba kwamitin hadin gwiwa na kungiyoyin biyu wato SSANU da NASU sun umurci mambobinsu da su shiga yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai kan rashin biyansu albashin watanni hudu da suke bin gwamnati bashi.

Gwamnan Akwa Ibom ya ki a sanya kwai a jerin kayan abincin da za a saukaka farashin su

 Gwamnan Akwa Ibom ya ki a sanya kwai a jerin kayan abincin da za a saukaka farashin su

Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya ki amincewa da bukatar a sanya “kwai” a cikin kayan abincin da gwamnatin jihar za ta sayar wa marasa galihu a kan farashi mai rahusa.

 Gwamnan ya nuna kin amincewa ne a yayin wani gagarumin taron Majalisar Zartarwa na Jiha, inda ya sanya hannu kan dokar kafa hukumar saye da sayarwa.

 ‘Yan Najeriya na fuskantar mawuyacin hali yayin da farashin kayan abinci ya yi tashin gwauron zabi bayan cire tallafin man fetur da shugaba Bola Tinubu ya yi.

APC ta zabi Idahosa a matsayin mataimakin gwamnan Edo a zaben da yake gabatowa

 APC ta zabi Idahosa a matsayin mataimakin gwamnan Edo a zaben da yake gabatowa.

Jam’iyyar (APC) ta tsayar da Hon. Dennis Idahosa a matsayin mataimakin dan takarar gwamna a zaben gwamnan Edo da za a yi ranar 21 ga watan Satumbar shekarar da muke ciki.

Shugaban jam’iyyar APCn na kasa, Abdullahi Umar Ganduje da sakataren jam’iyyar na kasa, Sen. Ajibola Bashiru za su gabatar da Sanata Monday Okpebolo, a matsayin dan takarar gwamnan da kuma abokin takararsa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a villa dake Abuja.

Idahosa shine ya maye gurbin Hon. Omoregie Ogbeide-Ihama wanda dan takarar gwamnan ya bayyana a makon da ya gabata a matsayin abokin takararsa.

Jaridar Nation ta rawaito cewa Idahosa, dan majalisar wakilai, an tabbatar dashi a daren ranar Lahadi bayan wani dogon zama da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar Edo, da shugabannin jam’iyyar da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima suka yi.

Sheikh Ibrahim Khalil ya bukaci gwamnan Kano ya bada murja kunya a matsayin mataimakiya ta musamman.

 Shahararren Malamin Addinin Musulunci ya bukaci Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya nada, Murja Kunya a matsayin mai Taimakawa gwamnan ta musamman a Social Media.

Sanannen malamin addinin musulunci, Sheihk Ibrahim Khaleel, ya bukaci gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya nada , Murja Ibrahim Kunya yar Tik Tok,a matsayin babbar mataimakiya ta musamman kan kafafen sadarwa na zamani.

Sheikh Khalil ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadin da ta gabata a cikin wani shiri da yagabatar a tashar Freedom Radio da ke Kano.

Malamin yace yin hakan zaitamakawa gwamnati da al’umma kwarai da gaske wajen,tallafawa mata musamman yan social media ta yadda za’a fito da sabbin hanyoyin kasuwanci na zamani da zai taimaka ta shafukan sada zumunta.

A kwanakin baya ne Hukumar hisbah ta jihar kano ta gurfanar da murja Ibrahima a gaban wata kotun shari’ar Musulunci  karkashin jagorancin Nura Yusuf Ahmad ta bayar da umarnin cewa, Murja Ibrahim Kunya a kaita asibiti domin ayimata gwajin tabin hankali a wani asibitin gwamnati domin sanin halin da take ciki.

Har yanzu Nijar ba ta bude boda ba

Nijar ta hana a tsallaka iyakarta, sa’o’i 72 bayan sanar da bude boda kasar da Nijeriya kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito
Har ya zuwa yanzu dai hukumomin Jamhuriyar Nijar din ba su ce uffan ba game da wannan mataki na gwamnatin Nijeriya.
Hukumomin Nijeriya irinsu na Kwastam da na kula da shige da fice na Immigration, sun sassauta hanyoyin shiga da fitar, amma na Jamhuriyar Nijar ba su yi hakan ba.
A ranar 13 ga watan Maris din nan dai ne fadar shugaban Nijeriya ta sanar da bude iyakokin kasa da na sararin samaniya ga Jamhuriyar Nijar tare da janye mata takunkuman da aka kakaba mata tun bayan da aka samu samu juyin mulki da ya yi sanadiyyar hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum Mohammed.

Farashin kayan abinci ya ki sauka duk da rahusar da Dala ta fara yi a Nijeriya

Farashin kayan abinci ya kara kara ta’azzara a makon farko na azumin Ramadana, domin kuwa a makon jiya, masara ta fi sauki a kasuwar Kashere da ke jihar Gombe, inda ake sayar da buhun kan kudi ₦56-57,000, amma a wannan makon kudin buhun masarar ya koma ₦58,000.

 
To a kasuwar Mile 12 International Market Legos ma kudin Buhun Masarar a makon nan ₦68,yayinda a makon daya shude ake saidawa Kan kudi ₦65,000.
Haka nan a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa, masarar ta fi sauki a makon da ya gabata, a makon jiyan dai, an sayar da buhun masarar akan kudi ₦53-55,000, amma a yanzu da ke cikin watan Ramadan kuwa buhun masarar ya koma ₦58,000 har zuwa N60,000.
 
Ko da ya ke a iya cewa Masarar ta yi zarra a kasuwar Mai’adua jihar Katsina, a wannan makon da ke shirin karewa, an sayar da buhun masarar ₦64,000 a kasuwar.
Da alama a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, kudin buhun masarar bai sauya ba daga na satin da ya shuɗe, domin a wancan makon an sayar da buhun kan kudi ₦58,000, to haka batun yake a wannan satin ma.
Ita ma dai kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna, farashin buhun masarar bai sauya tufafin shi na makon da ya gabata ba, an sayar da masarar kn kuɗi ₦57,000 haka kuwa farashin ya ke a makon da ke shirin yi mana ban kwana.
A bangaren shinkafa kuwa, ‘yar gida ta yi tashin gwauron zabi a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, domin kuwa a makon nan an sayi shinkafar kan kudi ₦130,000, inda aka samu karin ₦10,000 kan na wancan makon da aka saya ₦120,000 cif-cif.
 
A Kasuwar Kashere da ke jihar Gombe kuwa a satin can an sayar da buhun shinkafar Hausar kan kudi Naira ₦115,000-120,000, a makon nan kuwa kuɗin ₦120,000-130,000 ne.
Hakazalika,a kasuwar Mai’adua jihar Katsina ma an sayi buhun tsabar shinkafar Hausa ₦130,000 daidai.
Da muka leka kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa kuwa, mun tarar da cewa shinkafar Hausar ta fi sauki a makon da ya shude sama da wannan makon, a gabataccen makon an sayi shinkafar ₦120,000, amma a makon nan an samu karin ₦7,000, inda aka sayar ₦127,000.
Sai dai an samu sauƙin farashin shinkafar gida a kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna da a makon da ya gabata ake sayar da shinkafar gidan ₦130,000, yayin da a satin nan kuwa aka sayar da ita kan kuɗi ₦128,000.
A ɓangaren shinkafar bature kuwa, ta fi tsada a makon da ya shude, inda ake sayar wa kan kuɗi ₦75,000 a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa, amma a makon nan ₦72,000 ne kuɗin buhun shinkafar.
Sai dai batun yasha banban dana Kasuwar Mile 12 International Market Legos,domin kuwa kuɗin Buhun Shinkafar waje ₦83,000 ne saɓanin na baya da ake Sayar wa ₦75,000.
A kasuwar Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe kuwa, shinkafar waje tafi sauki a makon da ya gabata,an dai sayar da buhun shinkafar ₦80,000 a makon, yayin da a wannan makon kuɗin buhun ya kai ₦82,000-85,000
Shinkafar ‘yar waje ta fi tsada a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano a makon nan, ana sayar da buhun shinkafar ₦87,000, yayin da a makon da ya ke karewa kuwa ake sayar da da shi kan kudi ₦85,000.
 
Haka nan an samu sassaucin ₦2000, a kasuwar Giwa ta jihar Kaduna a makon nan, an sayi shinkafar ₦78,000, amma makon da ya shude ₦80,000 ne kuɗin buhun shinkafar baturen.
To bari mu kammala Farashin kayakin abinci na wannan makon da Taliyar Spaghetti, kwalin taliyar ya fi tsada a makon nan da ke shirin karewa a kasuwar Giwa ta jihar Kaduna, ana sayar wa kan kuɗi ₦15,000 dai dai, yayin da a makon da ya wuce aka sayar ₦14500,haka nan batun yake a kasuwar Mile 12 International Market Legos,kudin Kwalin taliyar ₦15000 daidai a wannan makon.
Amma a kasuwar Kashere da ke jihar Gombe kuma kuɗin Spaghetti ya ɗan sauka,inda ake sai da wa ₦13,100, saɓanin na baya da aka sayar ₦13,200.
To a kasuwannin jihohin Katsina ,Kano da Adamawa dai, farashin kwalin taliyar 13,500 ne a makon nan, haka kuma aka sai da a makon da ya shude ma.
DCL HAUSA A’isha Usman Gebi

Kwastam sun mika wasu motoci 6 makare da abinci ga masu kayan

 

Kwastam sun mika wasu motoci 6 makare da abinci ga masu kayan

Hukumar Kwastam ta Jihar Katsina ta hannanta wasu manyan motoci guda shida makare da kayan abinci ga masu su kamar yadda Shugaba Bola Tinubu ya ba su umurni.

Motocin da aka mika su ga masu su an tare su ne a shingen binciken kan iyakar Kongolam da ke karamar hukumar Mai-Adua a jihar Katsina.

Shugaban ya bayar da umurnin ne da nufin tabbatar da an samu wadatar abinci da kuma rage wahalhalun da akasarin ‘yan kasar ke fuskanta.

Jam’iyyar PDP na son a yi bincike kan zargin cushen N3.7trn a kasafin 2024

 Jam’iyyar PDP na son a yi bincike kan zargin cushen N3.7trn a kasafin 2024

Jam’iyyar adawa ta PDP a Nijeriya ta bukaci a gudanar da bincike kan zargin cushen kudi N3.7trn a kasafin kudin 2024.

Jam’iyyar ta PDP ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Debo Ologunagba ya fitar a Abuja.

Ologunagba ya ce binciken zai taimaka wajen gano abubuwan da suka sa aka dakatar da Sen.  Sanata Abdul Ningi (PDP-Bauchi) da Majalisar Dattawa ta yi, yana mai cewa an dakatar da Ningi ne ba tare da yin cikakken bincike kan kasafin kudin da ake zargin sa ba.