Thursday, April 9, 2026
Home Blog Page 453

An samu Gidauniyar da ta yi karo-karon kudi sama da Naira Milyan 140 don tallafa wa gajiyayyu cikin watan Ramadan a Kano

Gidauniyar Peace Ambassadors Association, ta tattara kudi daga cikin mambobinta da suka haura Naira milyan 140 don su sayi kayan abinci, sutura da kudi tsaba da za su rarraba ga mabukata masu karamin karfi a jihohin arewacin Nijeriya.
Daya daga cikin mambobin kungiyar Amb Usman Muhammad Maliya ya ce sun sayi madara katan 300 da 
Indomie katan 300 da kuma buhunan shinkafa 300.
Sauran kayan da suka saya don rarrabawa su ne taliya katan 300 da 
Macaroni katan 300.
Sannan Amb Usman Muhammd Maliya ya ce sun sayi shaddoji da yadukan da za su raba wa iyalan mabukata da kuma kudi tsaba da duk za su rarraba don saukaka rayuwa musamman duba da halin da ake ciki.

Gwamnatin Kebbi ta rage sa’o’in aiki ga ma’aikatan gwamnatin jihar

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnatin jihar a cikin wannan watan na Ramadan.

Kwamishinan ma’aikatar fansho da horaswa na jihar Auwal Manu-Dogondaji ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a yau Talata.

Ya ce matakin zai baiwa ma’aikatan gwamnati damar gudanar da ibada cikin sauki.

Majalisar dattijai ta dakatar da Sanata Ningi bisa zargin karkatar da kasafin kudi

Majalisar dattijai ta dakatar da Sanata Ningi bisa zargin karkatar da kasafin kudi

Majalisar dattijai ta dakatar da Sanata Abdul Ningi na tsawon watanni uku bisa zargin cusa Naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Ningi shi ne shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da yawan al’umma kuma yana wakiltar Bauchi ta Tsakiya.

Akwai yiyuwar sojojin Nijar su saki Bazoum a Azumin nan

 Akwai yiyuwar sojojin Nijar su saki Bazoum a Azumin nan

 Gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar ta ce a shirye take ta amince da sakin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum da matarsa ​​Khadija.

Majiyoyi da dama a Nijeriya da makwabciyarta Nijar, sun tabbatar da shirin gwamnatin mulkin soja na sakin hambararren shugaban kasar a cikin ‘yan kwanaki nan na watan Ramadan.

Sai dai an gano cewa babban abin da ke damun manyan jami’an soji a jamhuriyar Nijar shi ne nacewar Bazoum na cewa zai ci gaba da zama a cikin kasar ta Nijar, bisa dalilin cewa ba ya sha’awar komawa wata kasa daban don ci gaba da rayuwa.

Bazoum na samun goyon bayan shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, sannan kuma shugaban Najeriyar kuma jagoran kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), Bola Tinubu.

‘Yan bindiga sun nemi a ba su kudin fansa Naira tiriliyan 40 da babura 150 a Kaduna

 ‘Yan bindigar da suka yi garkuwa da mutane 16 a unguwar Gonin Gori da ke wajen garin Kaduna na Nijeriya sun nemi kudin da suka zarta hankali, inda a wannan Litinin manyan unguwar suka ce maharan da suka kwashi mutanen unguwarsu a ranar 28 ga watan Fabrairun da ya gabata sun nemi a ba su naira tiriliyan 40 ( kusan sau 2 na kasafin kudin kudin Nijeriya na 2024) da motocin Hilux 11 da kuma babura 150 a matsayin kudin fansa domin su sako mutanen na Gonin Gora.

 

Gwamnan Kano ya roki Tinubu da ya bude boda

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya roki shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu da ya bude boda domin a samu wadatar abinci a Nijeriya baki daya. 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar ban girma da shugaban hukumar kwastam, Adewale Adeniyi, ya kai masa ranar Litinin a Kano.

Gwamna Abba Kabir-Yusuf, ya koka kan mawuyacin halin da ‘yan Najeriya ke ciki sakamakon matsi da tattalin arzikin kasar ke ciki, ya ce sake bude iyakokin zai taimaka wajen magance hauhawar farashin kayayyaki da kuma saukar da farashin su.

NiMet ta yi hasashen za a yi rana a wasu jihohin Nijeriya

 NiMet ta yi hasashen za a yi rana a wasu jihohin Nijeriya

 Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya, NiMet, ta yi hasashen hasken rana da jin dadi daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar.

 An fitar da hasashen yanayi na NiMet ranar Lahadi a Abuja, inda aka yi hasashen yanayi za a iya samun yanayi na rana daga ranar Litinin a yankin arewa.

A cewarta, ana sa ran samun gizagizai tare da hasken rana a jihohin Arewa ta Tsakiya da ake sa ran za a iya samu yanayin tsawa a sassan jihar Benue da safiyar Laraba.

‘Yan bindiga sun kwashi almajirai masu yawa a Sokoto

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1cfziUmhVg1hQbYlcyClQPulucFNnuIzM

‘Yan bindiga sun kwashi almajirai daga wata makarantar Allo da ba a san iyakarsu ba a Sokoto.

Shugaban makarantar tsangayar da ke kauyen Gidan Bakuso a karamar hukumar Gada Liman Abubakar ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa kawo yanzu ba su ga almajirai 15 tun bayan farmakin na ‘yan bindigar na Asubahin Asabar din nan.

Gwamnan Katsina Dikko Radda ya umurci a zaftare farashin kayan abinci daga rumbun gwamnati saboda azumi

Gwamnan jihar Katsina, Dakta Dikko Umaru Radda ya bada umurnin a soma sayar da MASARA da GERO da DAWA na Gwamnatin Jiha, ga jama’a akan Naira Dubu Ashirin kowane buhu.
Gwamna Dikko Radda ya bada umurnin hakan ne a yau Jumu’a, 8/3/2024 jim kadan bayan ya kaddamar da babban Kwamitin rabon hatsi da dafaffen abinci na jiha da kuma na kananan hukumomin 34 na jihar Katsina, a dakin taro na gidan gwamnati.
Bayanin Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ofishin Sakataren Gwamnatin jihar Abdullahi Aliyu Yar’adua da DCL Hausa ta samu kwafi a Katsina.
Ya yi bayanin cewa gwamnatin jiha ta sayi buhu Dubu Saba’in da Biyu da Dari Biyu na masara da gero da dawa inda za a kai buhu Dari Biyu a kowace Mazaba 361 dake fadin jihar nan.
Dakta Dikko Umaru Radda ya kara da cewa an kayyade cewa za a iya sayar adadin da buhu daya ne kadai ga gungun Mutum Biyar.
Gwamnan ya kuma ce gwamnati ta kammala tsarin shirin rarraba dafaffen abinci kyauta ga mabukata tun daga ranar daya ga Watan Ramalan mai kamawa har zuwa karshensa in Allah Ya kai mu.
 A karkashin wannan shiri, Malam Dikko Radda ya ce an yi tanadin rarraba ingantacen abinci domin buda baki ga Mutum Dubu Saba’in da Biyu a kowace rana, a cibiyoyi dandaban da za a bude a ko’ina cikin fadin jihar Katsina.
Hakan ya nuna cewa ta wannan sabuwar hanyar da aka kirkiro, gwamnatin jihar Katsina za ta ciyar da jama’a mabukata sama da Miliyan Biyu a cikin Watan nan mai alfarma dake tafe.
Bugu da kari kuma, Gwamna Dikko Umaru Radda ya sanar cewa gwamnatinsa ta tanadi buhun shinkafa mai cin kilo 25, wanda za a raba kyauta ga Mutane Dubu Talatin Da Uku (masu bukata ta musamman da gajiyayyu da tsofaffi marasa sukuni).
Gwamna Dikko Radda ya yi bayanin cewa gwamnatin jihar Katsina ta dauki wadan nan matakai ne don kokarin karya farashin abinci, wanda ya yi tashin gwabron zabo, da kawo sauki ga al’umma, da kuma ciyar da abinci ga masu rauni a cikin Watan Azumi dake tafe, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Don haka, ya yi gargadin cewa dukkan shirye – shiryen an tanade su ne domin talakawa masu bukata, don haka kada a ga wani mai sukuni na kokarin saye, ko shiga layin amsar abinda za rarraba ma masu rauni.
Saboda haka ya bukaci wakilan Kwamitocin da aka kafa da su sanya ido sosai, su tabbatar an yi adalci a wajen aiwatar da wadan nan aiyuka kamar yadda gwamnati ta tsara don amfanin talaka.
 Ya kuma yi kira ga daukacin al’umma da su bada hadin kai da goyon baya ga Kwamitocin domin a samu nasara.
Babban Kwamitin na jiha wanda ke karkashin jagoracin Malam Halilu Musa Kofar – Bai, na da wakilan masu martaba Sarakunan Katsina da Daura, da wakilan Kungiyoyin Izala da Darika, da Kungiyoyin farar hula da Dr Bashir Ruwangodiya da Dr Ahmad Filin Samji da PPS, Abdullahi Aliyu Turaji da shugaba da Sakataren Jam’iyyar APC na jiha da Imam Samu Magaji Bakori.
 A jawabinsa, shugaban Kwamitin na jiha, Malam Halilu Musa Kofar- Bai, ya yi godiya ga Allah da yaba ma Gwamna Dikko Umaru Radda akan kirkiro da wannan shiri a lokacin al’umma ke cikin mawuyacin hali. Ya kuma yi fatar cewa za a sanya ido a ga abinda shi da daukacin abokan aikinsa za su aiwatar.

Fursuna ya kwace bindigar Gandiroba ya harbi wani mai faci a Kwara

 

Fursuna ya kwace bindigar Gandiroba ya harbi wani mai faci a Kwara

Wani fursuna a gidan yari da ke Oke-Kura a Ilorin babban birnin jihar Kwara ya yi kukan kura ya kwace bindiga hannun jami’in tsaron gidan yari ya harbe wani wani mai sana’ar faci a gefen hanya.

Hakan ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da aka fitar da wasu fursunonin gidan yarin.

Lamarin dai ya faru ne misalin karfe 8:00 na safe, kuma ya haifar da firgici da fargaba yayin da mazauna yankin suka tarwatse domin samu tsira a yayin faruwar qbin wanda ya yi kama da wasan kwaikwayo.

Nan take aka garzaya da mai facin zuwa wani asibiti domin kula da lafiyarsa aka kuma ci gaba da tsare wannan fursuna da ya yi aika-aika.