‘Yan bindiga sun hallaka Kwamandan jami’an sa kai na ‘Community Watch Corp’ a jihar Katsina
Ma’aikatan Jihar Neja sunfara yajin aikin sai Baba tagani.
Ma’aikatan Jihar Neja sunfara yajin aikin sai Baba tagani.
Kungiyar kwadago a jihar Neja ta sanar da daukar matakin fara yajin aiki na masana’antu wanda zai fara aiki daga ranar Laraba 21 ga Fabrairu, 2024.
A cikin wata wasika da ta aikewa gwamnatin jihar Neja ta ofishin sakataren gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar shugaban kungiyar NLC na jihar Idris A. Lafene da shugaban kungiyar TUC na jihar Ibrahim Gana.
matakin zai cigaba har sai gwamnati ta warware duk wata takaddamar da ke tsakaninta da kungiyar kwadago ta jihar.
Kungiyar kwadagon ta bukaci gwamnatin jihar da ta sauya duk wasu nade-naden siyasa a matsayin manyan daraktocin kudi, ayyuka da gudanarwa na hukumomi.
Haka kuma ta bukaci gwamnati da ta sauya nadin shugabanni da mambobi da kwamishinonin dindindin na hukumar ma’aikatar kananan hukumomi da na hukumar da kuma nadin manyan daraktoci na wasu hukumomi.
Za a hukunta ‘Yansandan da ke amfani da sunan IGP wajen aikata ba daidai ba.
Za a hukunta ‘Yansandan da ke amfani da sunan IGP wajen aikata ba daidai ba.
Babban Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya yi kakkausar suka ga duk wani nau’i na karbar kudi tare da yin gargadi ga duk wani jami’in da ya yi amfani da su ko kuma a sakaya sunansa wajen aikata miyagun ayyuka.
Jaridar SOLACEBASE ta ruwaito cewa Sufeto Janar din ya nuna matukar damuwarsa, inda ya jaddada cewa irin wannan aika-aikar na zubar da mutuncin sa da kuma rundunar ‘yan sandan Nijeriya, wanda hakan ke zubar da mutuncin jama’a.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Laraba.
IGP din ya jaddada cewa duk wani jami’in da aka samu da laifin yin amfani da sunansa da laifin zamba ko karbar kudi zai fuskanci hukunci mai tsanani. Daga nan sai ya bukaci jami’an da su tabbatar da gaskiya da sanin ya kamata, yana mai jaddada cewa mutuncin rundunar ‘yan sandan Nijeriya na cikin hadari idan ba a duba irin wannan ba, ‘’in ji sanarwar.
Gwamnatin Dikko ta dora harsashin gina jihar Katsina yadda ya kamata – Bala Abu Musawa
Hukumar kwastam ta bayyana shirinta na raba kayan abinci ga yan Najeriya
Dangane da halin kunci da ake fama dashi a Najeriya, hukumar kwastam ta bayyana shirin ta na raba kayan abinci da da hukumar ta kama ga ‘yan Najeriya.
Shugaban Hukumar Bashir Adewale Adeniyi, ya ce za a raba kayan abincin ne bayan an tantance mutane.
Hakan dai na a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Maiwada ya fitar a yau Talata, Adeniyi ya jaddada aniyarsa na shirin samar da abinci kamar yadda shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniya.
‘Yan sanda sun tabbatar da mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai a jihar Katsina
‘Yan bindiga sun kai mummunan hari kusa da sansanin sojoji a Katsina
Nijar: Janar Tiani ya yi wa gwamnatinsa garanbawul
Nijar: Janar Tiani ya yi wa gwamnatinsa garanbawul
Shugaban gwamnatin rikon kwaryar mulkin sojan Nijar Janar ABDOURAHAMANE Tiana ya yi wa gwamnatin sa kwarya kwaryar garan bawul
Sakataren gwamnatin kasar ya bayyana hakan ta kafar talabejin din kasar
Kuma wannan garan bawul ya shafi ma’aikatu uku ne da suka hada da ta ma’adanai, ta man fetur da ta makamashi inda aka nada musu sabbin ministoci
ECOWAS na shirin dage takunkumin da ta sanyawa Nijar
ECOWAS na shirin
dage takunkumin da ta sanyawa Nijar
Kungiyar ECOWAS za ta dage wa Nijar takunkumin da ta labta mata tun bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yulin 2023
Jaridar Jeune Afrique ce ta ruwaito hakan inda ta ce wasu daga cikin ministocin kasashen Afirka ta Yammar ne suka shaida mata hakan
Wasu rahotanni na cewa dai a ranar 24 ga watan nan na Febarairu ne kungiyar za ta gudanar da wani taro wanda a yayin sa ne za ta cire wa Nijar din takunkumin tattalin arzikin




.jpeg)

.jpg)