Wednesday, April 8, 2026
Home Blog Page 465

Matashi mai shekaru 35 ya yi wa tsohuwa mai shekaru 55 fyade har ta mutu

Kotun Majistare da ke zamanta a birnin Akure na jihar Ondo ta tsare wani matashi mai shekaru 35 mai suna James Emmanuel bisa zargin yi wa wata tsohuwa mai kimanin shekaru 55 mai suna Deborah Abiodun fyade har ta mutu.
‘Yan sanda dai ne suka kama matashin bisa zarginsa da wannan aika-aika ga matar da take abokiyar aikinsa a ranar 17 ga watan Janairun, 2024 a yankin Oke-Edu na jihar.
Jaridar Punch ta rawaito cewa bayan James ya yi wa matar fyade, tana magashiyyan, ya rotsa mata dutse a kai, ya yasar da gawarta cikin juji.
Kotun dai ta umurci da a cigaba da tsare James a gidan gyaran hali, har sai ranar 27 ga watan Maris, 2024.

Kotun koli ta tabbatar da nasarar cin zaben gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Fintiri

0

 

Alkali John Okoro wanda ya yi shari’ar jihar Kano ne ya tabbatar da nasarar ta Fintiri inda ya ce watsi da karar Aishatu Binani ta jam’iyyar APC

Atiku ya soki Tinubu kan matsalar tsaro a Nijeriya.

 Atiku ya soki Tinubu kan matsalar tsaro a Nijeriya 

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya caccaki shugaban kasa Bola Tinubu kan gazawarsa wajen magance matsalar tsaro a kasar.

Atiku, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya mayar da martani ne kan yawaitar sace-sacen jama’a da kashe-kashen da ake yi a fadin kasar nan.

Atiku ya bayyana damuwar sa kan dalilin da ya sa shugaban kasar ya fara wata ziyarar sirri a kasar Faransa a daidai lokacin da ‘yan fashi da makami da sauran matsalolin tsaro dake kara samun wajen zama a kasar.

Gwamnatin Nasarawa ta musanta sanya hannu wajen kafa kungiyar ’yan banga ta Fulani a jihar.

 Gwamnatin Nasarawa ta musanta sanya hannu wajen kafa kungiyar ’yan banga ta Fulani a jihar.

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya bayyana cewa gwamnatin jihar ba ta da hannu wajen kafa kungiyar ’yan banga ta Fulani da aka kafa kwanan nan a jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ‘yan majalisar dokokin jihar karkashin jagorancin kakakin majalisar, Danladi Jatau domin taya shi murna bisa samun nassara da yayi a kotun koli a fadar gwamnatin jihar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da inganta zaman lafiya a jihar,inda jaddada cewa tuni jami’an tsaro na gudanar da bincike kan lamarin ‘yan banga na Fulani.

Ya ce da a ce matakin daga gwamnati ne, da an aika da kudirin dokar ga majalisar dokokin jihar domin tantance wa saboda haka basuda wata masaninya akan kaddamar da yan bangar.

NDLEA ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar kwayoyi a Kano.

 NDLEA ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar kwayoyi a Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, reshen jihar Kano, ta ce ta kama wasu mutane 198 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi tare da tarwatsa mahadar da ake tattaruwa don safarar miyagun kwayoyi guda 21 a Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kakakin hukumar a jihar Kano Sadiq Muhammad-Maigatari ya raba wa manema labarai a Kano.

Ya ce an kama su ne a tsakanin 17 zuwa 26 ga watan Janairu, a cikin shirin hukumar na “Operation Hana Maye” da Kwamandan Hukumar Abubakar Idris-Ahmad ya kaddamar domin yaki da shaye shaye.

A cewarsa, daga cikin mutane 198 da aka kama, 177 maza ne, 21 kuma mata ne.

Sojojin sama na bin hukumar zaben INEC bashi a Nijeriya.

 Sojojin sama na bin hukumar zaben INEC bashi a Nijeriya. 

Shugaban hafsan sojin saman Nijeriya Air Marshal Hassan Bala Abubakar, ya bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar (INEC) da ta biya wasu basuka da sojojin na sama ke bin ta.

Abubakar Hassan ya yi wannan kiran ne a Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin tawagar gudanarwar hukumar ta INEC, karkashin jagorancin shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, da suka ziyarci hedikwatar rundunar sojin sama.

 Yace ya yi amfani da wannan dama domin tunatar da shugaban INEC cewa akwai kudaden sojojin samar ke bin hukumar INEC da ya kamata a ce an biya.

Kuma biyan wannan kudaden zai ba rundunar ta sojin sama damar, ci gaba da gudanar da ayyukanta cikin walwala da kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Zulum ya umurci ciyamomin kananan hukumomi su rika sanya hannu a rajistar zuwa aiki.

 Zulum ya umurci  ciyamomin kananan hukumomi su rika sanya hannu a rajistar zuwa aiki 

Gwamnatin jihar Borno ta ce za ta  samar da na’urar daukar bayanai ga shugabannin kananan hukumomin jihar. 

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya umarci shugabannin kananan hukumomin da su zauna a yankunansu inda ya bukace su da su sanya hannu a rajistar zuwa aiki a kullum domin tabbatar da kasancewarsu a wuraren aikinsu.

Zulum ya ba da umarnin ne a Maiduguri, babban birnin jihar, yayin da ya jagoranci bikin rantsar da zababbun shugabannin kananan hukumomi 27.

Gwamnan ya umurci ma’aikatar kananan hukumomi da ta gaggauta tura na’urorin daukar bayanai na biometric zuwa kananan hukumomin domin shugabanninsu su rika buga babban yatsa a kullum da karfe 8 na safe, na rana, 2 na rana ko kuma karfe 3:30pm.

Ya ce matakin ya zama dole domin duba rashin zuwa aiki ko kuma kauce wa aiki da kowane shugaba ba tare da dalili na gaske ba kamar yadda wasu yi a baya.

Gwamnan ya bayyana cewa yadda ake samun ingantaccen tsaro a fadin jihar, akwai bukatar shugabannin kananan hukumomin su kasance tare da jama’arsu domin tallafa wa kudirin gwamnatinsa na gyara, sake ginawa, da kuma tsugunar da ‘yan gudun hijira a jihar inda

ya bukace su da su sarrafa karancin albarkatun kananan hukumomin bisa adalci da rikon amana.

Ba mu karbi takarda a hukumance daga kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso ba – ECOWAS

Kungiyar kasashe masu tattalin arziki ta ECOWAS ta ce har yanzu ba ta karbi wata sanarwa ko takarda a hukumance da ke nuna sun fice daga cikin kungiyar.
A cikin wata sanarwa daga sakatariyar kungiyar ta ce kawai abin da ta sani shi ne tana aiki ba gajiyawa wajen maido da kasashen bisa turbar dimokradiyya.
Ta sanar cewa har yanzu kasashen na da matukar amfani a tafiyar da lamurran kungiyar.
A ranar Lahadin nan dai, kasashen uku na Mali, Nijar da Burkina Faso suka sanar cewa sun fice daga kungiyar ta ECOWAS inda suka ce ana musu barazana. Kasashen uku dai na karkashin jagorancin sojoji bayan da suka hambarar da gwamnatin farar hula.

Ba mu kulla yarjejeniya da kowa ba gabanin hukuncin kotun koli – Gwamnan Kano Abba

0

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya musanta cewa ya kulla wata yarjejeniya da fadar shugaban kasa gabanin hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar 12 ga watan Janairun 2024.

Bayanin hakan na acikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Tofa ya fitar yau Litinin.

A yayin da yake mayar da martani kan wata takarda da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani, wadda ke nuni da cewa akwai yarjejeniya tsakanin Gwamnan da fadar shugaban kasa a matsayin wani sharadi na samun nasara a shari’a a kotun koli.

Jaridar DCL Hausa ta ruwaito a ranar 20 ga watan Satumba, kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamnan jihar Kano ta kori Abba Kabir Yusuf, na jam’iyyar NNPP.

Bayan ɗaukaka ƙara a kotun Koli a ranar 12 ga Janairu, ƙotun ta yi watsi da hukuncin da ƙananan kotuna suka yanke na korar gwamnan a bisa kujerar sa.

Ɗalibai 8,285 za su zauna a jarabawar WASSCE ta farko da kwanfuta.

0

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta sanar cewa ɗalibai 8,285 ne a fadin ƙasarnan suka yi rajista domin fara jarrabawar kammala karatun sakandare a wannan shekarar ta 2024.

Ofishin shugaban hukumar na kasa Amos Dangut ne ya sanar da hakan a yau Litinin a wani taron manema labarai, inda ya ce za a gudanar da jarrabawar daga ranar 31 ga watan Janairu zuwa 17 ga watan Fabrairu.

Shugaban ya kara da cewa, kimanin dalibai 3,949 maza ne, wanda ke da kashi 47.66 cikin 100, yayin da 4,336 mata ne, wanda ke da kashi 52.3 cikin 100.