An kama shugaban jam’iyyar PDP da ake zargi da safarar makamai zuwa jihar Zamfara
Zargin kisan kai ya sa an tsare shugaban karamar hukuma gidan yari a Katsina
Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani
Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce ba shi da niyyar ficewa daga jam’iyyar sa ta (NNPP) da ya ci zabe a karkashinta.
Gwamna Abba ya bayyana hakan ne kwana daya bayan da shugaban jam’iyyar APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bashi goron gayyatar komawa jam’iyyar APC.
Gwamna Abba Kabir, wanda kotun koli ta tabbatar da shi a matsayin Gwamnan jihar Kano a ranar Juma’a 12 ga watan Janairu shi ne kadai gwamna a jam’iyyar NNPP a Nijeriya.
A yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ya gudana a Kano, Ganduje ya yi kira ga Gwamna Abba Kabir tare da mambobinsa da magoya bayansa na jam’iyyar NNPP da su sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matakin kasa domin tabbatar da ci gaban siyasar jihar Kano.
Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON.
Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON
Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya roki ‘yan wasan Super Eagles da su yi duk mai yiwuwa don ganin sun samu nasara a yayin da Najeriya zasu fafata da babbar abokiyar hamayyarta, Kamaru a gobe, domin buga wasan dab da na kusa da na karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Cote d’Ivoire. .
An isar da sakon shugaban kasar ga tawagar ta hannun ministan raya wasanni, Sanata John Owan Enoh, inda ya bukaci Super Eagles da su jajirce wajen tunkarar abokan karawarsu a wasan zagaye na 16 mai mahimmanci na gobe asabar.
Kamar yadda wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiya ta musamman ga sanata Enoh, Diana-Mary Tiku Nsan, ta bayyana cewa ‘yan Super Eagles sun sanar da cewa shugaban kasar na bin kungiyar ne domin yayi duk abinda ya dace a kansu, don haka dole ne su rubanya kokarinsu domin ‘yan Nijeriya da suke gida su samu Farin ciki da wannan wasa .
‘Yan Nijeriya na bukatar cikakken bayani kan bashin Dala bilyan 3.3 na kamfanin NNPC.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin tarayya kan bashin gaggawa na dala biliyan 3.3 na biyan danyen man fetur, Inda yabayyana cewa yan Nijeriya na bin gwamnati bayani akan batun bashin.
Atiku ya bayyana hakanne a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a abuja inda yake cewa kamata yayi gwamnati ta dunga fito da bayanai da al’ummar kasa zasu fahimta bawai tayi shiru ba.
Gwamnatin tarayya dai tun a shekarar da ta gabata, 16 ga watan Agusta, 2023, ta samu lamuni ta hannun kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) domin bayadda bashin dala biliyan 3.3.

.jpeg)




