Buhari ya gaza samar da tsaro a tsawon shekaru, Tinubu na neman nanata irin kuskuren – Peter Obi
‘Yan siyasa ne ke dagula harkokin zabe a Nijeriya – Ganduje
Tinubu ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na farko a 2024
Za a kashe N32bn don kwaskwarima ga ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro
Kimanin watanni 8 kenan da gina katafaren ginin da a yanzu haka hukumar kula da harkokin tsaro ta kasa ta ware Naira biliyan 31.915 a cikin kasafin kudin shekarar 2024 domin yin sabbin gine-gine.
Wannan dai ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun yawaitar kashe-kashe da sace-sacen al’umma a wasu jihohin Nijeriya, ciki har da babban birnin tarayya Abuja, inda ‘yan bindiga ke sace jama’a daga gidajen su da wuraren kasuwancinsu.
A ranar 21 ga Maris, 2023, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya kaddamar da katafaren ginin ofishin harkokin tsaron na kasa da Cibiyar Yaki da Ta’addanci ta Kasa (NCTC), wadanda suka lakume biliyoyin Nairori.
A lokacin da yake kaddamar da wasu cibiyoyi guda biyu na zamani a Abuja, ya ce an yi su ne don inganta da magance matsalolin tsaro a kasar nan, musamman ta’addanci ayyukan bata gari.
Sabbin gine-ginen suna dauke da manya-manyan ofisoshi tareda babban dakin taro da cibiyoyin nazari da bincike.
Wani fasinja ya gartsawa ma’aikaciyar Jirgi cizo.
Fasinja ya gartsa wa ma’aikaciyar jirgin sama cizo
Wani jirgin sama a kasar Japan da ke kan hanyarsa ta zuwa Amurka ya koma birnin Tokyo bayan da wani fasinja da ya bugu da giya ya ciji wata mata ma’aikaciyar jirgin da hakan ya tilasta wa matukin jirgin saukar gaggawa.
An ruwaito cewa mutumin mai shekaru 55 da ake kyautata zaton Ba’amurke ne, ya ciji matar a hannunta, inda har ya ji mata rauni, kamar yadda mai magana da yawun kamfanin All Nippon Airways ya shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP.
Lamarin da ya sa matukan jirgin da fasinjoji 159 suka zuwa filin jirgin Haneda, inda aka mika mutumin ga ‘yan sanda.
Kafar yada labarai ta kasar Japan TBS ta ruwaito fasinjan yana fadawa masu binciken cewa “bai san ya aikata laifin ba”.
Gwamnatin Kano zata kashe Biliyan 8 wajen gina makarantun firamare 3.
Gwamnatin jihar Kano za ta kashe N8bn a makarantun firamare guda 3.
Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan 8 domin gina manyan makarantun firamare guda uku a fadin jihar.
A cewar Gwamna Abba kabir Yusuf, makarantun za su kasance da cikakkun wuraren karatu, wanda hakan zai ba da isasshen yanayi ga yaran da suka fito daga sassa daban daban da zasuyi karatu a makarantun don samun ingantaccen ilimi da samun ci gaba.
Gwamnan ya ce za a samar da manyan makarantun ne a Yankuna Uku dake jihar kuma za’a samar da kayayyakin koyo na zamani don samar da ingantaccen Ilimi a makarantun.
Ya kuma ce an ware naira biliyan 6 domin gyara dukkan makarantun firamare dake jihar.
Yace gwamnati ta amince da gyara wasu cibiyoyi na musamman guda 26 da tsohon Gwamna Rabi’u Kwankwaso ya kirkiro dasu a lokacin gwamnatin sa kuma an kammala 17.
“Za mu ci gaba da ba da kulawa ga samar da kayan aikin koyarwa na yau da kullum dazai ba wa yaranmu damar samun ingantaccen yanayin koyo da koyarwa a jihar kano.


%20(15).jpeg)



%20(14).jpeg)
%20(12).jpeg)
