Tuesday, April 7, 2026
Home Blog Page 474

An samu Gwamna a Nijeriya da ya kiyasta kashe N702m kan abinci da nishadi

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya saka Naira milyan 702 a matsayin da za a kashe wajen sayen abinci da kuma samar da nishadi a ofishinsa da na Sakataren Gwamnatin jihar.
Gwamnan ya ware wadannan kudaden ne a cikin daftarin kasafin kudin shekarar 2024 kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.
Kwamishinan tsare-tsaren kasafin kudi Ademola Adeleke wanda ya tabbatar da labari a lokacin kare kasafin kudi, ya musanta cewa an ware Naira bilyan 11 don biyan wadannan bukatun.
Kwamishinan ya ce an ware Naira bilyan 8 don gudanar da ayyukan yau da kullum a ofishin Gwamna da sassan da ke karkashin ofishin.

EFCC na neman iznin kamo tsohuwar ministar jin kai a gwamnatin Buhari, Sadiya Umar Faruq

Jami’an hukumar hana yi wa tattalin arzikin kasa tu’ammati EFCC na duba yiwuwar neman takardar iznin kamo tsohuwar ministar jin kai a gwamnatin Buhari, Sadiya Umar Faruq.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa hakan ya biyo bayan kin amsa goron gayyatar da hukumar ta yi mata a ranar Laraba.
Sadiya Umar Faruq dai da hukumar ta shirya karbar bakuncinta da misalin karfe 10 na safiyar Laraba, ana tuhumarta da batun wasu kudi da suka kai darajar sama da Naira bilyan 37.
Ana dai zargin cewa an wawure wadannan kudaden a zamanin da take minista ta hannun wani dan kwangila Mr James Okwete.

‘Ya’ya da jikoki ne kadai za su iya biyan bashin da ake bin kasashen Afrika – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce irin tarin bashin da ake bin kasashen Nahiyar Afrika, ‘ya’ya da jikoki ne ya kamata su mayar da hankali wajen biyan wannan bashin.
Tsohon shugaban kasar ya ce, idan aka yi la’akari da wannan bashin, babu abin da ya dace a yi a nan gaba, illa a biya don ceto Nahiyar daga halin da ba a fatar ta shiga.
Obasanjo ya ce bashin da gwamnatinsa ta ciyo na Paris Club, gwamnatin da ta gaje shi ba ta ririta shi yadda ya kamata ba. Ya kara da cewa hakan ya jefa kasar cikin mawuyacin hali.
Ya ce bashi wani dodoridi ne da ake yi wa kasashen Afrika, amma dai ya ce shugabanci ne babbar matsalar kasashen Nahiyar Afrika.

Gwamna Dauda zai tallafi manoma dubu 100,000 a jihar Zamfara.

 Gwamna Dauda zai tallafi manoma dubu 100,000 a jihar Zamfara 

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada kudirin gwamnatinsa na tallafa wa manoma da inganta harkar noma a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin kaddamar da shirin farfado da tattalin arzikin Najeriya na Coronavirus Action tare da rarraba kayan amfanin gona da kadarorin noma.

Bikin wanda aka gudanar  da shi a ma’aikatar noma ta jihar,  ga wadanda suka amfana daga kananan hukumomi 14 na jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ya kuma rabawa Manema Labarau a birnin Gusau.

Ya ambato gwamnan yana cewa “Ta hanyar shirin FADAMA III, manoma 100,000 ne za a basu kayan aiki da iri a cikin shekaru hudu masu zuwa.

“Yace Kamar  yadda al’umma suka  sani, shirin COVID-19 Action farfadowa da na’ura da kuma Tattalin Arziki Shirin shiri ne da ya kunshi bangarori daban-daban da ke kewaye da yankuna uku masu mahimmanci kuma an tsara shi don magance  ƙalubale da damar yin amfani da damar kan hanyar zuwa ingantacciyar rayuwa bayan annoba.

“A karkashin Shirin FADAMA 111, yankin da aka fi mayar da hankali kan samar da wadataccen abinci da tabbatar da ingantaccen tsarin samar da abinci ga gidajen Al’umma masu rauni.

Hukumar Hisbah a jihar Kano takama mota dauke da barasa

 Hisbah a Kano ta kama mota makare da barasa 

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta sanar da kama wata babbar mota makare da kwalaben barasa.

Hukumar ta kama motar a hanyar Zariya, ta kuma kama direban motar da wasu mutane biyu. 

Babban Daraktan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Alhaji Abba Sufi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Malam  Ibrahim-Fagge ya sanya wa hannu a Kano.

“ Yace Motar da ke dauke da kwalabe daban-daban na barasa sama da 24,000 an kwace daga hannun ‘yan sumogal a hanyar Zariya da tsakar dare.

Jami’an Hisbah a jihar sun himmatu wajen yaki da shan miyagun kwayoyi da fasakwaurin barasa da sauran abubuwa masu sa maye a cikin jihar.

Sadiya Umar Faruq za ta gurfanar a gaban EFCC

Tsohuwar minista jin kai a lokacin mulkin Shugaba Buhari Sadiya Umar-Farouq za ta gurfana a gaban jami’an hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) bisa zargin almundahanar kudi har naira biliyan 37.
A makon jiya ne dai EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar domin ta amsa tuhume-tuhume da ake yi mata lokacin da ta ke rike da mukami.
Ana tuhumar ta kan zurarewar wasu kudade kimamin N37,170,855,753.44 da ake zargin an karkatar da su a yayin da ta ke jagorancin ma’aikatar ta jin kai.
Jami’an hukumar yaki da cin hanci da rashawa sun shaida wa wakilin majiyar DCLHausa ta Daily trust a ranar Talata cewa, an bukaci tsohuwar ministar ta bayyana a gaban masu bincike a hedikwatar hukumar ta EFCC da ke Jabi, Abuja, da karfe 10:00 na safiyar Larabar nan.

Jerin jami’o’in kasashen ketaren da Nijeriya ta dakatar da amincewa da su

0
NUC

Gwamnatin tarayya ta sanar da dakatar da jami’o’in kasashen waje su 18 a Najeriya a wannan Talata. Ga jerin sunayen jami’o’in kasashen waje da Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta dakatar, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

 1. Jami’ar Kimiyya da Gudanarwa, Port Novo, Jamhuriyar Benin, da sauran cibiyoyinta a Najeriya.

 2. Kwalejin Jami’ar Volta, Ho, Volta Region, Ghana, da sauran cibiyoyinta a Najeriya.

 3. Jami’ar International University, Missouri, USA, Kano da Lagos, ko kuma wani cibiyoyi da ke Najeriya.

4. Jami’ar Columbus, UK, tana aiki a ko’ina a Najeriya.  

5. Tiu International University, UK tana aiki a ko ina a Najeriya.  

6. Jami’ar Pebbles, UK tana aiki a ko’ina a Najeriya.

7. London External Studies UK tana aiki a ko’ina a Najeriya.

 8. Jami’ar Alhazai tana aiki a ko’ina a Najeriya.

 9. Jami’ar Kirista ta yammacin Afirka tana aiki a ko’ina a Najeriya.

10. EC-Council University, USA, Ikeja Lagos Study Centre.

 11. Concept College/Jami’o’i (London) Ilorin ko wani daga cikin cibiyoyinta a Najeriya.

 12. Jami’ar Houdegbe ta Arewacin Amurka da ke Najeriya.

13. Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Irish London, tana aiki a ko’ina cikin Najeriya.

 14. Jami’ar Ilimi, Winneba Ghana, tana aiki a ko’ina cikin Najeriya.

 15. Jami’ar Cape Coast, Ghana, tana aiki a ko’ina a Najeriya.

 16. African University Cooperative Debelopment, Cotonou, Benin Republic, yana aiki a ko’ina cikin Najeriya.

 17. Jami’ar Yammacin Pacific, Denver, Colorado, Cibiyar Nazari Owerri.

 18. Jami’ar Evangel ta Amurka da Chudick Management Academic, Legas.

Gwamnan Kano ya dora wa ma’aikata N20,000 a albashinsu don rage radadin tsadar rayuwa

0

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano dora wa ma’aikatan gwamnati N20,000 kan albashinsu domin rage masu radadin cire tallafin man fetur.
‘Yan fansho kuma ya ba su kyautar N15,000.
Jaridar Leadership ta ruwaito shugaban kungiyar kwadago ta TUC a jihar Kano Comrade Mubarak Buba Yarima na cewa karin zai fara aiki daga watan Disambar 2023 har zuwa nan da watanni shida.

 

‘Yan sandan Katsina sun kuɓutar da mutane 171 daga hannun ‘yan bindiga a 2023

0
CP Aliyu Abubakar Musa

Rundunar yan sanda jihar Katsina tace ta kuɓutar da mutane 171 waɗan da yan bindiga suka yi garkuwa dasu a jihar.

Mai magana da yawun rundunar Yan sandan jihar Katsina, SP Sadiq Abubakar ne ya bayyana hakan a hedikwatar rundunar.

Abubakar yace rundunar ta samu nasarori a shekarar dubu biyu da ashirin da uku data gabata, ta kama mutane 1627, ta miƙa mutane 855 a gaban kuliya.

Haka zalika rundunar tayi nasarar kama mutane 258 bisa zargin su da aikata laifukan sata a jihar.

Tinubu ya dakatar da shugabar shirin NSIPA Halima Shehu

0

 

Halima Shehu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Halima Shehu, ko’odinetar shirin da ke kula da harkokin zuba jari ta kasa, sakamakon almubazzaranci da kudade.

Wannan na zuwa ne bayan watanni biyu da Majalisar Dattawa ta tabbatar da ita a matsayin kodinetan NSIPA na kasa.

Idan za’a tuna cewa a ranar 12 ga Oktoba 2023, shugaba Tinubu ya amince da nadin Halina Shehu.

Bayan dakatarwar da bincike kan zargin, an nada Dr Akindele Egbuwalo, Manajan Shirye-shiryen N-POWER na kasa a matsayin NC/CEO, har sai an kammala binciken.