Tuesday, April 7, 2026
Home Blog Page 479

Da N800 muke ciyar da duk kare daya da muke aiki da shi, yayin da muke ciyar da fursuna da N750 a kowace rana – Gwamnatin Nijerya

Shugaban hukumar kula da gidajen yari ta kasa Halliru Nababa ya ce hukumar na kashe kudi masu yawa don ciyar da karnukan da ake aiki da su, fiye da yadda ake kashe wa mutanen da ke tsare a gidan yari.
Halliru Nababa ya sanar da hakan ne a gaban kwamitin majalisar dokokin Nijeriya da ke kula da harkokin cikin gida son kare kasafin kudin shekarar badi, 2024.
Ya ce hukumar ta rubuta wa ministan harkokin cikin gida, inda take neman da a kara yawan kudin da ake ciyar da ‘yan gidan yari daga Naira 750 zuwa 3,000 a rana.
Shugaban hukumar ya ce har yanzu su na jiran amincewar ma’aikatar harkokin cikin gida kan wannan bukata ta su, inda ya bukaci majalisa ta sa baki don a amince musu su yi wannan karin.
Halliru Nababa ya ce a shekarar 2023, Nijeriya na da mutane 81,354 da ake tsare da su a gidajen ysrin kasar.
Hukumar ta sanar cewa tana ciyar da duk kare daya da ake aiki da shi a hukumar kan kudi Naira 800 duk rana.

Kotu ta yi hukunci ga mutumin da ya kashe abokinsa saboda Naira 100 a Zamfara

Babbar kotun jihar Zamfara ta yanke hukuncin kisa ga wani mutum mai suna Anas Dahiru bisa samunsa da laifin kashe abokinsa saboda takaddamar kudi N100.
A shekarar 2017 ne dai aka gabatar da Anas a gaban kotun, inda ake zarginsa da kisan abokinsa Shamu Ibrahim kan Naira 100, inda ya daba masa wuka.
Da ya ke karanta hukuncin, Alkalin kotun Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u, ya ce wanda ake zargin Anas Dahiru da ke a unguwar Dallatu da ke cikin birnin Gusau ya caka wa abokinsa Shamu wuka a lokacin da suke takaddamar kudi Naira 100.

Shugaba Tinubu bai saka aikin samar da lantarkin Mambila cikin kasafin kudin 2024 ba

Jaridar Daily Trust ta gano cewa a cikin daftarin kasafin kudin shekarar badi, 2024 d shugaba Tinubu ya gabatar wa majalisa, babu kason aikin samar da lantarki a Mambila da ke Gembu jihar Taraba.
Sai dai an ware wa ma’aikatar makamashi da ke kula da sha’anin lantarki kudi Naira milyan 400 don shirya taruka a cikin shekarar ta 2024.
Aikin samar da lantarki na Mambila dai ya haddasa ce-ce-kuce a zamanin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, da ake kyautata zaton idan an yi shi zai samar da megawatts 3,050 ga Nijeriya.
A shekarar 2017, majalisar zartarwar Nijeriya ta amince da fitar da kudi Dalar Amurka 5.729 kwatankwacin Naira Tiriliyan 1.140 don gudanar da aikin.

ECOWAS ta dorawa sojojin kasashen Nijar, Mali, da Burkina Faso alhakin karuwar ta’addanci a yammacin Africa

0

Kungiyar kasashen yammacin
Africa ta ECOWAS ta zargi sojojin da suka yi juyin mulki a kasashen Nijar, Mali
da Burkina Faso a matsayin wadanda ke rura wutar ta’addanci a nahiyar


Shugaban majalisar
gudanarwar kungiyar Omar Tourey ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi
wajen bikin bude taron kungiyar kan tsaro da shiga tsakanin rikice-rikice karo
na 51 da aka fara a Abuja.

Tourey ya ce juyin mulkin
da sojojin suka yi, ya rusa duk wani tsari ko kokari da kungiyar ke yi na
tabbatar da tsaro a yankin.

Ya kuma kara da cewa jan
kafar da sojojin ke yi wajen mika mulki hannun farar hula na baiwa ‘yan ta’adda
da masu daukar nauyin su kara azama wajen kaddamar da hare-hare kan fararen
hula.


Tourey ya kuma nuna
takaicin sa kan yadda sojojin ke amfani da juyin mulkin wajen yada farfaganda
irin ta siyasa yayin da suke nunawa duniya cewa zaluntar su ake yi.


Kididdiga ta nuna cewa juyin mulkin da
sojoji suka yi a wadannan kasashe ya jefa jama’a kusan miliyan 5 cikin yunwa da
bakin talauci, sai wasu miliyan 2.5 da suka rasa muhallan su, inda ya tilasta
rufe makarantu fiye da dubu 9.

 

Gwamnan Kano ya umurci Abdullahi Musa ya kula da ofishin SSG

0
https://drive.google.com/uc?export=view&id=1h4mmNfT8qSDNpAxGvJn4ZN2wlsxmP6t8
Gwamnan Kano Enge Abba Kabir Yusuf ya umurci shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Abdullahi Musa ya kula da ofishin sakataren gwamnatin jihar. Bayanan da DCL Hausa ta tattaro daga majiyoyi a gwamnatin ta Kano sun ce Abdullahi Musa zai kula da ofishin kafin sakataren gwamnati Abdullahi Baffa Bichi ya samu koshin lafiya. Sai dai Majiyar Ta DCL ta ce hakan ba ya nufin cewa an sauke sakataren gwamnatin jihar ta Kano.

Majalisar wakilai ta umarci jami’an tsaro su kama gwamnan babban bankin kasa

0

 Majalisar wakilan
Najeriya ta baiwa jami’an tsaro umarnin kama gwamnan babban banki CBN Mr Olayemi
Cardoso da Akanta Janar ta kasar Mrs Oluwatoyin Madein da karin wasu mutane 17,
sakamakon kin amsa gayyatar da ta yi musu a lokuta da dama.

Wannan umarni na
zuwa ne bayan bukatar hakan da dan majalisa Fred Agbedi daga jihar Bayelsa ya
mikawa majalisar.

Da yake karantowa majalisar muhimmanci kamo mutanen,
ya ce dabi’ar su ta kin girmama majalisar ya nuna irin girman kan da suke da
shi da kuma raina majalisa.

Don haka ne ya ce ya
zama dole majalisar ta yi amfani da karfin da take da shi wajen tursasa musu
gurfana a gaban ta, dalili kenan da ya sa kakakin majalisar Tajudden Abbas ya
umarci babban sufeton ‘yan sanda na kasa da ya kamo mutanen da kuma tabbatar
sun duka a gaban majalisar.

Majalisar
na bukatar su gurfana gaban ta don yi mata bayani filla-filla kan abinda zasu
yi da kudaden da aka ware musu a cikin kasafin kudin badi.

Adadin wadanda suka mutu a sanadin harin sojoji a Kaduna ya karu zuwa 120-Amnesty international

0

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty
International ta ce adadin wadanda harin bam din sojoji ya kashe a kauyen Tungar
biri na jihar Kaduna ya kai 120 zuwa yanzu.

Bayanai na nuna cewa har yanzu babu wani alamu a
aikace na daukar mataki kan sojojin da suka aikata wannan danyen aiki, in banda
Allah wadai da gwamnati ta yi.

Har ya zuwa yanzu dai akwai mutane fiye da 50 da ke
kwance rai a hannun Allah a asibiti suna karbar kulawar jami’an lafiya bayan
wannan abin takaici da ya rutsa da su.

Sai dai kuma adadin da Amnesty ta bayar ya ci karo
da wanda hukumar bayar da agaji ta kasa NEMA ta bayar wanda ke cewa kawo yanzu
mutane 85 ne suka mutu a sanadin harin, yayin da 66 suka jikkata.

Wannan dai ba shi ne karon farko da jami’an sojoji
ke hallaka mutane da sunan kuskure a arewacin Najeriya ba, inda kididdiga ke
nuna cewa ire-iren wadannan hare-hare sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani
ba har sama da 400 daga 2014 zuwa yanzu, musamman a jihohin Borno da Zamfara.

 

 

EFCC na bukatar gwamnatin tarayya ta ware sama da biliyan biyu don saya mata motocin alfarma a kasafin kudin badi

0

Hukumar dake yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya
na bukatar gwamnatin tarayya ta kara yawan kudaden da aka ware mata daga naira
biliyan 43 zuwa naira biliyan 76 a cikin kasafin kudin badi.

 

Wannan bukata na kunshe ne cikin wata takarda da
shugaban hukumar Ola Olukoyede ya mikawa kwamitin kudi na majalisar wakilan
kasa.

 

Takardar na kunshe
da bayanin bukatar siyawa hukumar sabbin motoci na akalla naira biliyan 2 da
miliyan 600 sai wasu karin naira biliyan 33 da hukumar ke son ayi mata.

Da fari dai an warewa hukumar naira biliyan 37 da gudanar da
ayyukan yau da kullum da kuma naira biliyan 4.7 don cike gibi idan bukatar
hakan ta taso da kuma naira biliyan 1.2 don gudanar da manyan ayyuka.

Jaridar Premium
times ta ruwaito tun kafin shugaban kasa ya gabatarwa majalisar kasafin kudin
badin hukumar ta EFCC ta gabatar masa da wannan kuduri nata, sai dai kuma
shugaban bai shigar da bukatar ba, saboda wani dalili nasa.

Da yake kara yiwa ‘yan majalisar jawabi kan bukatar kara yawan
kudin, Mr Olu yace akwai bukatar a wadata hukumar da kudi gudun kada rashin
kudade isassu a hannu ya sanya ta fada karbar cin hanci a maimakon yaki da shi.

 

 

 

Kotu ta umurci tsohon Gwamnan Zamfara Matawalle ya dawo da motocin gidan gwamnati

Babbar kotu da ke zamanta a Sokoto ta yi watsi da bukatar tsohon Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle kan hakkin mallakar motocin gidan gwamnati da ya tafi da su bayan ya sauka daga Gwamna a watan Mayun, 2023.
A watan Juni, ‘yan sanda sun shiga gidajen Matawalle suka kwaso motocin da ke ciki kamar yadda kotu ta umurta.
A cikin wata sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara Sulaiman Bala Idris ya sanar cewa kotu ta yi watsi da bukatar Matawalle a kan wadannan motoci.
Sulaiman Bala Idris ya ce tsohon Gwamnan na jihar Zamfara wanda yanzu haka shi ne karamin ministan tsaro a Nijeriya, shi da wasu jiga-jigan gwamnatinsa, sun kwashi motocin da aka ware wa ofisoshinsu suka bar gwamnatin Dauda Lawan babu motocin da za su yi amfani da su.
Sanarwar ta tunaso cewa duk a cikin watan Juni, gwamnatin Dauda ta ba Matawalle da saura mukarrabansa wa’adin kwanaki biyar na su maido da wadannan motoci. Ya ce bayan kin bin wannan urni ne ya sa gwamnati ta nemi iznin kotu ta je ta kwaso wadannan motoci.
Bayanai sun ce a baya, akwai kotun da ke zama a Gusau babban birnin jihar Zamfara, ta umurci da a maida wa Matawalle motocin, inda Matawalle ya sake shigar da wata kara yake neman kotun ta halasta masa wadannan motoci.
A haka ne, gwamnatin Dauda ta nemi a mayar da shari’ar a babbar kotu.

Nijar ta kulla yarjejeniyar tsaro da Rasha

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun rattaba hannu kan yarjejeniyar karfafa huldar tsaro da kasar Rasha.
A yayin wata ziyara ce da wata babbar tawagar kasar Rashar ta kawo Nijar ne karkashin jagorancin karamin ministan tsaron kasar manjo kanal Evkurouv Lunus-Bek aka kulla wannan wannan yarjejeniya tare da ministan tsaron Nijar janar Salifou Mody.
Daga bisani tawagar ta samu ganawa da shugaban gwamnatin mulkin sojan birgediya janar ABDOURAHAMANE Tiana a fadar sa.