Sojoji sun yi ikirarin yin sabon juyin mulki a Gabon
Nijar ta bukaci jakadanta da ke Faransa ya dawo gida
Rashin sanin tarihi zai sa ku tabka kuskure irin na magabata – Atiku
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya jaddada
muhimmancin ilimin tarihi wajen gina kasa. Maitamaki na musamman kan harkokin yada labarai ga Atikun ya ce Waizrin Adamawa ya ambata hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin ayarin
hukumar editocin jaridar The Sun karkashin babban editan ta Mr. Onuoha Ukeh
yayin da suka kai masa ziyara a gidan sa da ke Abuja a wannan Talata.
kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa a gaban kotu, kasancewar sa wanda ya
yiwa jam’iyyar PDP takara, ya ce ba tare da la’akari da darrusan da tarihi ya
nuna ba, za a ci gaba da maimaita kura-kuran da aka tafka a baya. Yace wadanda
suke zaune ba tare da sanin abin da ya gabace su ba, akwai yuwuwar su aikata
kura-kuran magabata, inda ya ce ba daidai ba ne a cire darasin tarihi daga
manhajar koyarwar makarantun Nijeriya.
Ruftawar gini ta yi ajalin mutane a sansanin ‘yan gudun hijira na Borno
Rahotanni daga birnin Maiduguri na cewa mutane 7 sun mutu a sakamakon faduwar gini a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke birnin Maiduguri na jihar Borno.
Jami’an kungiyar Civilian JTF sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa wani aji ne ya fado kan wasu mutane da ke kwana a ciki sanadin ruwan sama a garin Munguno.
Bayanai sun ce ginin ya fado ne da misalin karfe 7 da rabi na safiyar yau, kuma nan take mutane 7 suka ce ga garin ku nan.
Wasu jami’an lafiya sun tabbatarwa manema labarai cewa akwai mutane fiye da 20 yanzu haka da ke kwana a babban asibitin garin Munguno suna karbar magani bayan raunukan da suka gamu da su.
Garin Munguno da ke da nisan kilomita 85 zuwa birnin Maiduguri na da ‘yan gudu hijira fiye da dubu 40 wadanda suka gujewa ta’addancin Boko Haram daga garuruwan su.
Jam’iyyar NNPP ta dakatar da Rabi’u Musa Kwankwaso
Babbar kotun jihar Kano ta haramtawa EFCC da wasu hukumomi bincikar Muhuyi
APC ta bar ‘yan kasa cikin yunwa – PDP
Jam’iyyar adawa ta PDP a tarayyar Nijeriya ta soki lamirin salon mulkin gwamnatin Shugaba Tinubu ta ce sama da mutane milyan 150 a fadin kasar na kwana da yunwa.
Wannan dai ba bakon abu ba ne a siyasar kasar inda ko a lokutan baya lokacin da jam’iyyar APC ke adawa kafin darewa a kan madafun iko ta sha caccakar PDP dangane da salon jagorancinta.
Garin kwaki ya yi ajalin wata budurwa a Kano
Wata Budurwa mai suna Fiddausi Mahmud da ke garin Rimin Hamza a karamar hukumar Tarauni a jihar Kano ta mutu a sakamakon cin garin kwaki da ta yi wanda ake zargin ya kulle mata ciki lokacin da take matsananciyar jin yunwa.
Gidan rediyon Rahama da ke Kano ya ruwaito cewa mahaifin Fiddausi, Malam Mahmud Abdullahi ya ce iyalansa sun kwashe tsawon yini guda ba samu abincin da za su ci ba abin da ya sa ya fita nema kuma ya yi dace ya samo musu garin kwaki. Magidancin ya ce ba ya samun abin da ya wuce Naira 500 a rana guda, lamarin da ya kara jefa rayuwar iyalansa cikin wani mayuwacin hali la’akari da tsadar rayuwar da ake fuskanta a Nijeriya bayan janye tallafin man fetur.
Rahotanni sun ce tuni aka yi janaizar marigayiya Fiddausi kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.
‘Yan Nijeriya sun yi ”wawa” a wajen rabon kayan tallafi
Wasu mutane a jihar Bayelsa da ke Najeriya sun fasa tare da wawushe rumbun tara hatsi da sauran kayan abinci da gwamnatin jihar ta killace a birnin Yenagoa domin raba wa jama’a da zummar rage radadin ibtila’in ambaliyar ruwa tun a 2022.
RFI Hausa wacce ta ruwaito wannan labarin ta ce gwamnatin jihar ta ce wasu daga cikin kayan abincin sun fara lalacewa.
An fasa rumbun ne da ke kan babbar hanyar Isaak Boro a Yenagoa saboda irin tashin hankalin da al’umar ke ciki na hauhawar farashn kayayyakin masarufi wanda ya samo asali daga cire tallafin man fetur da ya haddasa tsananin tsadar rayuwa.
Janye tallafin ne ya sa farashin man fetur ya yi tashin goron-zabi daga N190 zuwa 620 kan kowacce lita wanda hakan ya shafi farashin motocin sufuri da kayan abinci da sauransu.
Sai dai Hukumar Agajin Gaggawa ta jihar Bayelsa ta bayyana cewa wadannan kayayyakin abincin da aka kwashe ba su da ingancin da za a iya aci, domin sun lalace don haka duk wanda ya ci zai fuskanci matsala.
Tinubu ya haramtawa wasu mukarraban gwamnati zuwa Amurka



