An kama barayin da suka saci agwagi da kare a Kano
An kama barayin da suka saci agwagi da kare a Kano
‘Yan sintirin Vigilante na garin Gurungawa dake karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano sun kama matasa hudu da ake zargi da satar wasu agwagi da wani kare.
Kwamandan kungiyar sintirin a garin Abdulhamid Dan’azumi ya ce jami’ansa sun ji motsin matasan da tsakar dare kusan misalin karfe 3 a lokacin da karnuka suka fara haushi a kansu. Bayan jami’an sun isa, suka tarar har sun hallaka kare daya.
Ya ce bayan kama matasan sun amsa laifinsu, kuma an kwace makamai da dama daga wajensu bayan da suka tabbatar da cewa sun dade su na aikata wannan assha.
Daya daga cikinsu, ya sanar cewa sun sa kudi sun sayi karen ne, amma dai agwagin ba na su bane, sun gansu ne suka kwashe suka zuba cikin buhu.
Kotu ta hana a tuhumi Hudu Yunusa-Ari
Kotu ta hana a tuhumi Hudu Yunusa-Ari
Babbar kotun tarayya dake Abuja ta hana hukumar zaben Nijeriya INEC tuhumar kwamishinan zaben da ya ayyana Sanata Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaben Gwamnan jihar Adamawa a zaben 2023.
Mai Shari’a Dotanus Okorowo ya yanke hukuncin hakan, bayan da lauyan Hudu Yunusa-Ari, wato Mr Michael Aondoaka ya bukaci hakan a gaban kotu.
Lauyan Hudu Yunusa-Ari ya shaida wa kotu cewa hukumar zaben INEC ba ta hurumin tuhumarsa har sai kotun sauraren kararrakin zaben ta sanar da makomar dakataccen kwamishina a hukumar zaben.
Amai da gudawa bai kama Alhazan Kano ba – NAHCON
Amai da gudawa bai kama Alhazan Kano ba – NAHCON
Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta musanta rade-radin da ake yadawa cewa amai da gudawa ta barke a daya daga cikin masaukan Alhazan jihar Kano dake birnin Makka na Saudi Arabia.
Shugaban tawagar likitocin hukumar NAHCON Dr Usman Galadima ya sanar da hakan a Makka, Saudi Arabia, inda ya ce gurbataccen abinci ne wasu daga cikin Alhazan suka ci daga hannun ‘takaru’ ya lalata musu ciki.
Ya ce an bude wani cibiyar kula da lafiya ta wucin-gadi a wurin da lamarin ya faru inda ake kula da lafiyar kusan Alhazai 9 da abin ya shafa bayan da suka ci dambu.
Dr Usman ya ce tun daren Asabar, bayan da aka tura tawagar likitoci a wurin, sun shawo kan lamarin, har ma an sallami wadanda suka kamu.
Shugaban tawagar likitocin ya ce duk da shawarwarin da aka ba Alhazan na su guji yame-yamen abinci musamman wanda ba a tabbatar da sahihancinsa ba, amma suka yi kunnen-kashi suka ci.
Wata jarumar fim ta mutu
Wata jarumar fim ta mutu
Jaruma a masana’antar shirya fina-finan Nollywood Sidikat Odukanwi ta mutu bayan fama da rashin lafiya.
‘Yar kabilar Yoruba Sidikat ta mutu, bayan fama da rashin lafiyar da ta tilast mata daina fitowa a fim na tsawon lokaci.
Diyar mamaciyar, Bisi Aisha ce ta sanar da mutuwar mahaifiyar tata da aka fi sani da Iyako Oko.
‘Yar asalin jihar Osun, an haifi Iyako a shekarar 1960.
Farashin fetur ya kusa linkawa a kasashen Kamaru, Benin da Nijar bayan cire tallafin man a Nijeriya
Bayanan da majiyar DCL Hausa ta Daily Trust ta samo sun nuna cewa farashin litar man fetur ya kusa linkawa a kasashen Kamaru, Benin da Jamhuriyar Nijar bayan da Nijeriya ta sanar da cire tallafin man fetur din.
Bayanan sun ce samun fetur din cikin rahusa, ya sa ‘yan kasuwa na ‘sumogal’ dinsa zuwa kasashe makwabta daga Nijeriya har a wuce da shi Sudan wadansu lokutta.
Hakan dai na ba ‘yan Nijeriya wahala wajen samun isasshen man da za su yi amfani da shi, da wasu lokuttan akan shiga matsalar karancinsa. Bayanai dai sun tabbatar da cewa cire tallafin man fetur din ya haddasa barazana ga tattalin arzikin kasashen makwabta da yanzu haka harkokin ‘bumburutu’ suka yi kasa.
Binciken jaridar ya gano cewa ana farashin ya koma CFA700 ko CFA800 a kasar Benin sabanin CFA450 da ake sayarwa kafin a cire tallafin man a Nijeriya.
A baya, ana sayar da litar fetur a Nijeriya kan kudi N195, a kasashe makwabta kuwa ana sayar da litar man kan kudi CFA508 kwantankwacin Naira 381. A haka ne ‘yan ‘sumogal’ ke amfani da damar domin fitar da shi, don a samu kazamar riba.
Rashin lantarki ya sa daliban jami’ar ABU daina karatu
Harkokin karatu sun samu tangarda a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya yayin da dalibai suka shafe kusan wata daya zaune a gida sakamakon matsalar wutar lantarki da jami’ar ta shiga.
A ranar 15 ga watan Mayun da ya gabata ne hukumar da ke dakon hasken lantarki ta yanke hanyar lantarki ta jami’ar sakamakon bashin da suke bin jami’ar.
Jaridar Daily trust ta gano cewa hukumar gudanarwar jami’ar ta biya kamfanin Kaduna Electric Naira miliyan 40 daga cikin kudin wutar lantarki da ake bin su.
Sai dai duk da haka kamfanin na Kaduna Electric bai mayar da lanyin lantarkin makarantar ba.
