Sunday, April 5, 2026
Home Blog Page 504

Sojoji sun kama tirela makare da makamai za a shigo da ita Nijeriya daga Mali

Sojojin Bataliya ta 192 da ke aiki karkashin 81 Div, sun kama wata tirela makare da alburusai da ake kokarin shiga da ita jihar Anambra ta Nijeriya daga kasar Mali.
Mai magana da yawun rundunar soji ta kasa Janaral  Onyema Nwachukwu ya sanar cewa an kama wanda ake zargi da safarar wadannan makamai mai suna Mr Eric Seworvor dan asalin kasar Ghana da direban motar.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu ya yi murabus daga mukaminsa

Shugaban jam’iyyar APC a Nijeriya Sanata Abdullahi Adamu ya yi murabus daga mukaminsa na shugabancin jam’iyyar.
Wasu majiyoyi, sun tabbatar wa da jaridar Daily Trust cewa Abdullahi Adamu, wanda tsohon Gwamnan jihar Nasarawa ne ya aike da takardar ajiye mukamin nasa a fadar shugaban kasa, gabanin dawowar Shugaba Tinubu daga kasar Kenya.
Sanata Adamu da ya zamo shugaban jam’iyyar APC na kasa a Maris 2022 bayan zaben shugabannin jam’iyyar, ya aike da takardar ta ofishin shugaban ma’aikata ba fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamilla da yammacin Lahadi.
Wasu majiyoyi sun sanar da majiyar DCL Hausa cewa Sanata Abdullahi Adamu ya gaggauta yin murabus ne bayan da ya jiyo cewa akwai wasu gungun mutane da ke neman yi masa ature.

Dan ‘sumogal’ ya kashe jami’in kwastam a Kebbi

Hukumar Kwastam ta Nijeriya NCS reshen jihar Kebbi, a ranar Lahadin nan ta tabbatar da kisan wani jami’inta mai suna Aminu Abdullahi da ake zargin wani mai safarar motoci ya yi a karamar hukumar Yauri ta jihar.
Kakakin hukumar, ASC Mubarak Mustapha, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Birnin Kebbi.
Ya ce: “Tuni hukumar kwastam reshen jihar ta Kebbi, ta jajantawa iyalan jami’in Aminu Abdullahi, wanda wani da ake zargin mai safarar mota ne ya kashe a lokacin da yake bakin aiki.

Kotu ta umurci DSS da ta saki Emefiele ko ta kai shi kotu

Babbar kotun Abuja da ke zama a Maitama, ta ba hukumar tsaron DSS wa’adin mako daya da ko dai ta kai dakataccen Gwamnan babban bankin CBN kotu ko kuma ta sake shi.
Idan zaku iya tunawa dai, Godwin Emefiele ya maka ofishin babban lauyan gwamnati da hukumar DSS bisa kamu da tsare shi da aka yi, inda ya yi zargin cewa hukumomin na yi masa bi-ta-da-kullin siyasa.

Ina sane da mawuyacin halin da ‘yan Nijeriya ke ciki inji shugaban kasa Bola Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin halin kuncin da talakawan kasar suka shiga ta dalilin cire tallafin man fetur, inda ya tabbatar da cewa an dauki matakin ne don kasar ta cigaba da kuma gina kyakkyawar rayuwa ga ‘yan kasa.

Shugaba Bola Tinubu da ya karbi bakuncin tsoffin gwamnoni 18 da suka yi zamani tare a shekarar 1999 ya ce akwai bukatar ‘yan Nijeriya su kara hakuri da halin da suke ciki.
Ya tabbatar da cewa an yi tsari mai kyau domin rarraba tallafin da zai rage radadin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Za a samu matan da suka dauki juna biyu ba tare da sun shirya ba kimanin 700,000 cikin shekarar 2023 a Nijeriya

Asusun tallafa wa yawan al’umma na majalisar dinkin duniya UNPF ya ce kalubalen da ake fuskanta wajen shirin tsarin iyali na iya kaiwa ga yawan samun cikin-shege da yawan zubar da cikin.

UNPFA ta sanar da hakan ne a cikin sakonta na bikin zagayowar ranar yawan al’umma ta 2023 da hukumar kidaya ta kasa ta shirya a Abuja.
Kwararra a kan lafiyar mata masu juna biyu Dr Adeela Khan ta ce gibin da ale samu na ba da tallafin kudi wajen aiwatar da shirin tsarin iyali ya tashi daga Dala milyan 25 ya koma Dala milyan 32 a shekarar 2023.
A ta bakin Dr Adeela, wannan gibin kudin zai sa a samu juna biyu 700,000 da ba a yi niyyar samunsu ba da hakan zai sa a haifi cikunna 300,000 kuma a zubar da cikunna 300,000 a shekarar 2023.

Ba kowace iyakar Nijeriya muka bude ba – Kwastam

Mukaddashin shugaban hukumar Kwastam Wale Adeniyi ya ce ba dukkanin iyakokin Nijeriya na tudu aka bude ba. 

DCL Hausa tattaro cewa a yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai ne a ranar Talata a fadar shugaban kasa da ke Abuje, babban jami‘in na Kwastam ya ce suna nazarin iyakokin da ya kamata a bude su da kuma wadanda bai kamata a bude ba.

Katsinawa za su san wadanda Dikko zai nada kwamishinoni a makon gobe

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda zai aike da sunayen wadanda zai nada mukamin kwamishinoni a gwamnatinsa ga majalisar dokokin jihar a makon gobe.

Sakataren Gwamnatin Jihar Arch Ahmad Musa Dangiwa ya sanar da hakan a lokacin da ya karbi bakuncin jami’an kungiyar ‘yan jarida ta kasa reshen jihar Katsina a ofishinsa.
Sakataren Gwamnatin ya ce tuni Gwamnan ya hada jerin sunayen mutanen da za a nada mukaman, abin da ya rage kawai shi ne a aike da su majalisa don tantancewa da zarar majalisar ta dawo hutu.
Ya ce majalisar ma ta hannun kakaki da mataimakinsa ta tabbatar da shirinta na karbar wadannan sunaye da zarar sun dawo hutu a makon na gobe.

Zan samar da tsaron da ko tsakar dare ‘yan Nijeriya za su iya fita harkokinsu inji sabon shugaban sojoji

Babban hafsan sojin kasa na Nijeriya Manjo Janar Taoreeq Lagbaja, ya ce karkashin jagorancinsa, sojoji za su gudanar da aikin samar da tsaron da zai sa al’ummomin dake Neja, Zamfara da sauran jihohin dake fama da matsalolin tsaro za su rika fita harkokinsu ko da karfe biyun dare ne ba tare da sun ji tsoron harin ta’addanci ba.

Janaral Lagbaja ya ce sojoji za su yi aiki sosai a dazukan Birnin Gwari na jihar Kaduna da na Dansadau a jihar Zamfara inda ke da maboyar ‘yan ta’adda, ta yadda za su rasa mafaka.
Babban hafsan sojin na magana ne a lokacin da ya karbi bakuncin Gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani a hedikwatar tsaro ta kasa.

An kama jirgin da ya shekara 12 yana satar danyen mai a Nijeriya

A Nijeriya kamfanin NNPCL ya sanar da kama wani jirgin ruwa makare da dayen mai da yawansa ya kai kimanin lita 800,000 da ake zargin na sata ne.

Garba Muhammad, mai magana da yawun hukumar NNPC, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja.
Garba ya bayyana cewa jirgin na dauke da lamba: 6620462, mallakin wani kamfanin Nijeriya ne mai suna HOLAB MARITIME SERVICES LIMITED RC813311.
Haka kuma binciken da aka yi kan ayyukan jirgin da yanzu haka yake a ofishin hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ruwa ta NNPCL ya nuna cewa, jirgin ya shafe shekaru 12 yana gudanar da wannan badakala.