Thursday, April 9, 2026
Home Blog Page 63

Tinubu ne ya sahale wa Amurka kai hari bayan Nijeriya ta ba da bayanan sirri – Gwamnati

0

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya amince a kai hare-haren sama da Amurka ta yi kan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

 

Ministan Harkokin Waje Yusuf Tuggar ya ce hare-haren hadin gwiwa ne tsakanin kasashen biyu, inda Najeriya ta bayar da muhimman bayanan sirri kuma an aiwatar da su ne bayan samun cikakkiyar amincewar shugaban kasa.

 

Tuggar ya jaddada cewa aikin bai sabawa ikon kasa ba kuma ba ya da nasaba da addini.

 

Gidan talabijin na Channels ya ambato shi ya ce Najeriya kasa ce mai addinai da dama kuma ta na hada gwiwa da abokan hulda irinsu Amurka ne domin yaki da ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

 

A cewar Amurka, an kashe ‘yan ISIS da dama a hare-haren, yayin da AFRICOM ta tabbatar da cewa an yi su ne tare da cikakken hadin kai da hukumomin Najeriya.

Majalisar wakilan Nijeriya ta umarci a duba tare da sake fitar da dokokin haraji

0

Majalisar Wakilai a Nijeriya ta ce ta fara duba dokokin gyaran haraji bayan korafe-korafen jama’a da zargin an sauya wasu sassan dokokin da aka riga aka wallafa a sanarwar da gwamnati ta ba jama’a.

 

Mai magana da yawun Majalisar Akin Rotimi, ya ce an kafa kwamitin da zai binciki yadda aka bi wajen tsara wa da kuma aiwatar da dokokin domin gano ko akwai kura-kurai, tangarɗa ko wani tsoma baki a tsarin majalisa da na gudanarwa.

 

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito Rotimi ya ƙara da cewa Majalisar ta umarci Akawun Majalisar a sake wallafa dokokin tare da fitar da sahihan kwafi-kwafi na abin da Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai suka amince da shi.

 

Wannan mataki ya biyo bayan zargin da ɗan majalisa Abdussamad Dasuki daga Sokoto ya yi cewa dokokin da aka wallafa sun bambanta da waɗanda aka tattauna kuma aka amince da su.

 

Lamarin da ya sa ƙungiyoyi da jam’iyyun adawa, da ma kungiyoyi irin su NLC da NBA na neman a dakatar da aiwatar da dokokin da aka shirya su fara aiki daga ranar 1 ga watan Janairu na 2026, duk da karewar da Gwamnatin Tarayya ke yi cewa dokokin za su inganta tsarin haraji da rage nauyi ga marasa ƙarfi.

Amurka ta yabawa gwamnatin Nijeriya bayan kaddamar da hari

0

Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana godiyarsa ga gwamnatin Najeriya bisa goyon bayan da ta bayar a yayin farmakin sama da aka kai kan sansanonin ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma.

 

Wannan na zuwa ne bayan rahotannin da suka ce Amurka ta kaddamar da babban farmakin soji kan kungiyoyin ta’addanci a ranar Alhamis.

 

A cewar wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta fitar, an kai hare-haren ne a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da ƙasashe abokanta, ciki har da Amurka domin dakile barazanar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi.

 

Sanarwar ta jaddada cewa ana aiwatar da dukkan matakan yaki da ta’addanci ne bisa kare rayukan fararen hula, mutunta ikon ƙasa, da tabbatar da tsaro da hadin kan al’umma ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

0

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take kundin tsarin mulki da rashin kyakkyawan tafiyar da majalisar.

’Yan majalisar sun sanar da haka ne a Gusau a daren Laraba, 24 ga Disamba, bayan taron haɗin gwiwa, inda suka ce shugabancin majalisar ya mayar da kansa tamkar reshen zartarwa ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal.

Sun bayyana cewa an dakatar da su “ba bisa ƙa’ida ba” kusan shekara biyu, lamarin da ya hana al’ummarsu wakilci, har suka tilasta kafa majalisa ta daban domin kalubalantar abin da suka kira ayyukan ba bisa doka ba.

’Yan majalisar da suka sauya sheƙar sun haɗa da Hon. Bashar Aliyu Gummi, Hon. Nasiru Abdullahi Maru, Barr. Bashir Abubakar Masama, Hon. Bashir Bello, Hon. Amiru Ahmad Keta da Hon. Muktar Nasir Kaura. Sun kuma nemi Majalisar Ƙasa ta binciki rikicin majalisar Zamfara, tare da zargin PDP da rikice-rikicen cikin gida da gazawar shugabanci.

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

0

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin gurfanar da shi kan zargin safarar kuɗi har Naira biliyan 4.6.

Mai shari’a Emeka Nwite ya bayar da umarnin ne a ranar Laraba, bayan EFCC ta kasa gabatar da Adamu domin karɓar tuhuma karo na biyu a gaban kotu.

EFCC ta zargi Adamu da kamfanin Ayab Agro Products and Freight Company Ltd da haɗa baki wajen safarar N4.65bn tsakanin Yuni da Disamba 2023, lokacin da yake reshen Manajan Polaris Bank a Bauchi, tare da wasu mutane biyu da ake nema ruwa a jallo.

Lauyoyin wanda ake tuhuma sun koka kan ci-gaba da tsare Adamu ba tare da gurfanar da shi ba, suna cewa hakan na shafar ayyukan gwamnati, musamman biyan albashin ma’aikata a jihar, yayin da kotu ta dage sauraron shari’ar zuwa ranar 30 ga Disamba.

Shugaba Tinubu bai sauya Femi Gbajabiamila daga mukamin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa ba – Bayo Onanuga

0

Fadar Shugaban Nijeriya ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Shugaban Ma’aikatansa, Hon. Femi Gbajabiamila, da Sakatarensa, Hakeem Muri-Okunola.

A wata sanarwa da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar 25 ga Disamba, ya ce labarin ƙarya ne tsagwaronsa, inda ya jaddada cewa Gbajabiamila na nan daram a kan muƙaminsa.

Sanarwar ta ƙara da cewa Hakeem Muri-Okunola ma yana nan a matsayinsa na “Principal Private Secretary”, tana mai kira ga ’yan Nijeriya da su yi watsi da labaran bogi, tare da gargaɗin kafafen yaɗa labarai su rika tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa.

Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi tir da harin da aka kai masallaci a Maiduguri

0

Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Nijeriya ta yi kakkausar suka kan harin kunar bakin wake da aka kai Masallacin Kasuwar Gomboru a Maiduguri, Jihar Borno, inda ta bayyana harin a matsayin dabbanci, rashin imani da kuma yunƙurin tada tsoro da rushe zaman lafiya.

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya mika ta’aziyyarsa ga gwamnatin Borno da Gwamna Babagana Umara Zulum, da iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata.

Yahaya ya ce kai hari wurin ibada babban laifi ne ga tunanin ɗan Adam da tsarkin addini, yana mai jaddada cewa irin wadannan hare-hare ba za su karya gwiwar Arewa ba, illa ma su kara dankon zumunci wajen yakar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi.

Hakazalika ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da shugabannin Borno da kada su karaya, tare da bukatar a kara tsaurara tsaro musamman a wuraren ibada da tarukan jama’a, musamman a lokutan bukukuwa, domin hana aukuwar irin wannan hari a gaba.

Babban hafsan rundunar sojin kasa ta Nijeriya ya yi alwashin inganta tsaro ta hanyar amfani da karfi ko akasin haka

0

Babban Hafsan Sojin ƙasa, Lt.-Janar. Waidi Shaibu, ya tabbatar cewa sojojin Nijeriya za su cigaba da aiwatar da ayyuka na karfi da akasin haka domin inganta tsaro a fadin ƙasar.

Shaibu ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da wata makarantar sakandare ta gwamnati mai azuzuwa 36 ta ‘Yan Mata da aka inganta a Maradun, Zamfara, a karkashin shirin na Musamman na Hadin Gwiwar Soji da Al’umma (Special Intervention Civil-Military Cooperation) na Maj.-Gen. Mamman Galadima.

A cewarsa, dangantaka tsakanin al’umma da sojoji dole ta kasance ta haɗin gwiwa domin mutane suna bukatar soji, kuma soji ba zai iya cimma burinsa ba ba tare da goyon bayan al’umma ba. Shaibu ya yi kira ga ‘yan ƙasa su cigaba da amincewa da sojoji tare da ba da goyon baya ga ƙoƙarinsu.

Har ila yau, Shaibu ya bayyana cewa irin waɗannan ayyuka na musamman suna nuni da yabo ga al’ummomin manyan hafsoshin soja, da kuma tallafawa jihohi wajen samar da muhimman ababen more rayuwa domin inganta rayuwar al’ummomin da ake amfana da su.

Kwankwaso ya bayyana masu digirin digirgir “Phd” 300 da Gidauniyar Kwankwasiyya ta samar a taronta na shekara-shekara

0

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya bayyana sama da masu digiri na uku (PhD) 300 da aka samar ta hanyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya a taron farko na shekara-shekara na masu cin gajiyar tallafin a Kano.

Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gadon da shugaba zai iya bari ga al’umma, yana mai cewa saka jari mai dorewa a fannin shi ne ainihin ma’aunin kyakkyawan shugabanci.

A jawabin da ya yi a taron a ranar Laraba, Kwankwaso ya ce wannan taro tarihi ne ga Jihar Kano da Nijeriya baki ɗaya, inda ya lura cewa taron ya ba da darussa kan shugabanci, dorewa, da hangen nesa, tare da jaddada cewa auna shugabanci ya kamata ya dogara ne kan tasirinsa mai dorewa ga rayuwar ‘yan ƙasa.

Kwankwaso ya kuma bayyana cewa bayan zaɓen 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da tallafin ɗalibai a ƙasashen waje, ya ɗauki nauyin ci-gaba da shirin ta hannun Gidauniyar Ci-gaban Kwankwasiyya.

Gwamnatin Kano ta haramta biyan haraji da tsabar kudi daga 1 ga watan Janairu

0

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2026, ba za a amince da biyan haraji da tsabar kuɗi ko takardar banki ba domin toshe ɓarnar kuɗaɗen shiga.

Babban Daraktan Hukumar Tara Haraji ta Jihar Kano (KIRS), Muhammad Abba Aliyu, ya ce amfani da fasaha ya sa kuɗaɗen shigar wasu hukumomi suka tashi daga N50m zuwa N500m, abin da ya sa aka yanke wannan shawara.

Wani masani kan haraji, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya ce haraji na da nufin samar da kuɗaɗen raya ababen more rayuwa, rage tazara tsakanin masu wadata da talakawa, da daidaita tattalin arziki.