Thursday, April 9, 2026
Home Blog Page 64

Gwamnatin Kano ta haramta biyan haraji da tsabar kudi daga 1 ga watan Janairu

0

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2026, ba za a amince da biyan haraji da tsabar kuɗi ko takardar banki ba domin toshe ɓarnar kuɗaɗen shiga.

Babban Daraktan Hukumar Tara Haraji ta Jihar Kano (KIRS), Muhammad Abba Aliyu, ya ce amfani da fasaha ya sa kuɗaɗen shigar wasu hukumomi suka tashi daga N50m zuwa N500m, abin da ya sa aka yanke wannan shawara.

Wani masani kan haraji, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya ce haraji na da nufin samar da kuɗaɗen raya ababen more rayuwa, rage tazara tsakanin masu wadata da talakawa, da daidaita tattalin arziki.

‘Yan sandan Nijeriya sun kama wani da ya tsere daga gidan gyaran hali da wasu masu manyan laifuka a wani samame mabambanta a fadin kasar

0

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta ce rundunarta ta musamman (STS) ta kama wani fursuna da ya tsere daga gidan gyaran hali da kuma wasu mutane 21 a jihohi daban-daban bisa zargin fashi da makami, garkuwa da mutane, satar shanu, satar mota, safarar miyagun ƙwayoyi da kwaikwayon jami’an tsaro.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya ce an kai samamen ne bisa sahihan bayanan sirri, inda aka ƙwato bindigogi shida ciki har da AK-47, AK-49 da LAR, tare da harsasai, motoci, babura da sauran kayayyakin laifi.

A cewarsa, daga cikin wadanda aka kama har da Ayo Abiodun, fursunan Kuje da ya tsere, da ake zargi da fashin wani jami’in soja, da kuma wasu mutane da ke da alaƙa da ’yan fashi da masu garkuwa da mutane a Kaduna, Abuja, Lagos, Ogun, Edo da Nasarawa.

Hundeyin ya ƙara da cewa bincike na ci-gaba, kuma za a gurfanar da dukkan waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike, yana mai jaddada kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya.

Shugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan harin da aka kai a masallaci – Kashim Shettima

0

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin rundunonin tsaro na musamman zuwa Maiduguri, Jihar Borno, domin kamo waɗanda suka kai harin bam a masallacin Al-Adum da ke kasuwar Gamboru.

Shettima ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, bayan harin da ya kashe mutane biyar tare da jikkata wasu a lokacin sallar magariba ranar Laraba.

A cewarsa, Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ya ba da umarnin ƙara tsaurara matakan tsaro a Borno, yana mai jaddada cewa gwamnati na aiki tare da hukumomin jiha da jami’an tsaro domin kare al’umma da muhimman gine-gine a Arewa maso Gabas.

Shettima ya ƙara da cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunkuri na tayar da zaune tsaye ba, yana mai tabbatar wa ’yan Nijeriya cewa za a hukunta masu hannu a harin bisa doka, tare da jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa.

Kungiyar kwadago ta bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da dokokin harajin da aka gurbata

0

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bukaci ’yan Nijeriya da su ƙi duk wata dokar haraji da aka ce an sauya ko an yi mata magudi.

Shugaban kungiyar, Joe Ajaero, ya bayyana haka a sakon Kirsimetinsa na 2025, yana mai cewa irin waɗannan dokoki na rusa amincewar jama’a.

Ajaero ya ce ya kamata a tabbatar da adalcin haraji, inda masu hali za su biya daidai gwargwado, yana mai cewa dokar da ke ɗauke da magudi ko ƙirƙira ba za a amince da ita ba.

A halin da ake ciki, kwamitin wucin-gadi na Majalisar Wakilai da ke binciken zargin sauye-sauye a dokokin haraji ya ce zai kammala aikinsa cikin gaggawa domin miƙa rahoto ga majalisar.

Malaman jinya ‘yan Nijeriya da ke aiki a Ingila sun kai su 16,000 in ji rahoton jaridar Punch

0

Akalla ma’aikatan jinya da ungozoma 16,156 ‘yan Nijeriya sun samu lasisin aiki a kasar Birtaniya tsakanin 2017 zuwa 30 ga Satumba, 2025, a cewar bayanan Hukumar Kula da Jinya da Ungozoma ta Birtaniya (NMC).

Rahoton ya nuna yadda matsalar “japa” ke ƙara kamari, inda ƙwararrun ma’aikatan lafiya ke barin Nijeriya zuwa ƙasashen da ke ba da albashi mai tsoka, damar ci-gaban aiki da kyakkyawan yanayin aiki. Wannan na jefa tsarin kiwon lafiyar Nijeriya cikin barazana, musamman a yankunan karkara.

NMC ta tabbatar da cewa zuwa ƙarshen Satumba 2025, akwai ma’aikatan jinya 16,156 da aka horas a Nijeriya a kundin rijistarta. A watan Maris 2025, adadin ya kai 15,421, ƙaruwa da kashi 4.8 cikin watanni shida. Nijeriya na cikin ƙasashe uku da ke kan gaba wajen tura ma’aikatan jinya zuwa Birtaniya, bayan Philippines da India.

Haka kuma, rahoton jaridar Punch ya ruwaito cewa, kididdigar 2025 ta nuna cewa ma’aikatan lafiya 43,221 ciki har da likitoci, masu jinya, ungozoma da masu gwaje-gwaje sun bar ƙasar tsakanin 2023 da 2024, lamarin da ke ƙara tsananta ƙarancin ma’aikata a tsarin lafiya.

Cin hanci da rashawa na boye irin albarkar da Allah Ya ajiye a Nijeriya in ji shugaban hukumar EFCC

0

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce cin hanci da rashawa na boye albarkar da Allah Ya yi wa Nijeriya tare da hana ƙasar cimma cikakken ci-gabanta.

Olukoyede ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Laraba yayin saƙon Kirsimetinsa ga ’yan Nijeriya, inda ya yi kira da a haɗa kai wajen yaƙar cin hanci da rashawa domin ƙasar ta samu ƙarfi da wadata. Ya ce cin hanci na daga cikin manyan matsalolin da ke hana albarkar rayuwa da Allah Ya tanadar wa ƙasa.

Ya kuma bukaci ’yan Nijeriya su rungumi ƙimomin da Annabi Isa (AS) ya koyar na soyayya, haske da fata yana mai cewa su ne ginshiƙan ciyar da ƙasa gaba.

Shugaban EFCC ya ƙara da kira ga jama’a su goyi bayan ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa hakan zai ƙarfafa fata da amincewa cewa Nijeriya za ta iya shawo kan ƙalubalen da ke gabanta.

Shugaba Tinubu ya taya Ganduje murnar cika shekaru 76

0

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, murnar cika shekaru 76 a ranar 25 ga Disamba.

Tinubu ya bayyana Dr. Ganduje a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren mai gudanarwa, wanda ya yi wa ƙasa hidima a mukamai daban-daban tsawon kusan shekaru 50, ciki har da zama mataimakin gwamna da gwamnan Jihar Kano na wa’adi biyu.

Hakazalika, ya ce yana matuƙar godiya ga zumunci da haɗin gwiwar da ke tsakaninsa da Ganduje, yana mai addu’ar Allah Ya ƙara masa lafiya da tsawon rai domin ci-gaba da yi wa Nijeriya da al’umma hidima.

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

0

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki da kalaman ƙiyayya da yaɗa ƙarya a kafafen intanet, suna mai cewa matakin ba shi da hujja.

Gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta saka haramcin ne a ranar Talata kan ’yan Turai biyar, ciki har da tsohon kwamishinan EU ɗan Faransa, Thierry Breton, bisa zargin takaita ’yancin faɗar albarkacin baki da kuma tsaurara dokoki kan manyan kamfanonin fasaha na Amurka.

Hukumar Tarayyar Turai ta ce tana yin Allah-wadai da matakin, tare da jaddada cewa ’yancin faɗar albarkacin baki muhimmiyar ƙima ce da Turai da Amurka ke rabawa. Ta kuma yi gargaɗin cewa za ta iya ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Rahoton Reuters ya ce lamarin na iya ƙara rarrabuwar kai tsakanin Amurka da wasu ƙasashen Turai kan batutuwan tsaro, kasuwanci, siyasa da dokokin kafafen sada zumunta, musamman bayan EU ta ci tarar dandalin X na Elon Musk kan karya wasu dokoki a intanet.

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

0

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa gwamnatinsa za ta cigaba da kare ’yanci da lafiyar kowa ba tare da la’akari da addini ba.

Tinubu ya bayyana haka ne a saƙon taya murnar Kirsimeti na shekarar 2025 da ya fitar a ranar Laraba, inda ya taya Kiristoci a Nijeriya da sauran sassan duniya murna, yana mai cewa Kirsimeti lokaci ne na tunani kan haihuwar Annabi Isa Almasihu da saƙon zaman lafiya, ƙauna da fata.

Tinubu ya ce saƙon Almasihu a matsayin jagoran zaman lafiya ya dace sosai a wannan lokaci da Nijeriya ke fuskantar ƙalubale iri-iri, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa na jajircewa wajen tabbatar da ’yancin addini da kare jama’a daga duk wani nau’in tashin hankali.

Haka kuma ya yaba da gudummawar da Kiristoci ke bayarwa wajen ci-gaban Nijeriya, yana mai kira da a yi amfani da lokacin Kirsimeti wajen ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin ’yan ƙasa.

Akwai bukatar dole sai ‘yan kwallon Super Eagles sun inganta wasansu matukar suna son nasara – Eric Chelle

0

Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar 2–1 da suka samu a kan Tanzania a ranar Talata, rahoton PUNCH Sports Extra.

A wasan da aka buga a Complexe Sportif de Fès, Morocco, Semi Ajayi ya zura kwallo bayan minti 36 daga bugun kusurwar Alex Iwobi, amma Tanzania ta daidaita wasan da Charles M’Mombwa kafin Ademola Lookman ya sake ba Nijeriya jagoranci. Duk da haka, ‘yan wasan Chelle sun nuna kwarin gwiwa a don kare nasarar.

Chelle ya yi sharhi kan wasan yana mai cewa, “Dole ne mu nazarci wannan nasara saboda mun yi abubuwa da dama a rabin farko wajen hare-haren kwallaye. Amma a rabin na biyu, mun baiwa Tanzania damar dawowa cikin wasan. Mun yi kuskure biyu.”

Ya ƙara da cewa, “Tabbas muna farin ciki da samun maki uku, amma a AFCON, abu mafi muhimmanci shi ne mu cigaba da inganta kowane wasa.