Jam’iyyar PDP ta soki Gwamnatin Nijeriya kan yadda ba ta sanar da ’yan kasar game da farmakin saman da Amurka ta kai a Arewa maso Yamma ba sai bayan shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa labarin.
Kakakin PDP, Ini Ememobong, ya ce ya dace gwamnati ta fara wayar da kan jama’a game da lamarin, maimakon jiran tabbatar da abin da ya riga ya yadu a kafafen yada labaran ketare.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito PDP na cewa tsarin sadarwar da ke barin ƙasashen waje su fara sanar da ayyukan tsaro a Najeriya na da matuƙar damuwa.
Sai dai Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa farmakin hadin gwiwa ne, inda Najeriya ta amince da shi tare da bayar da bayanan sirri, kuma Shugaba Bola Tinubu ya amince da harin.
