Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiPDP tsagin Turaki ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta inganta walwala da Jin...

PDP tsagin Turaki ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta inganta walwala da Jin dadin sojoji domin karfafa tsaron Nijeriya

Kwamitin Zartarwa na Kasa na jam’iyyar PDP, karkashin jagorancin Tanimu Turaki (SAN), ya bukaci Gwamnatin Nijeriya da ta fifita inganta walwala da jin dadin jami’ai da sojojin rundunar tsaro domin karfafa kwarin gwiwa da tsaron kasa.

Turaki ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, yayin da ake bikin Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026, inda ya jaddada cewa bayar da cikakken tallafi ga rundunar soji na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiyar Nijeriya.

Ya kuma bukaci Gwamnatin Nijeriya da ta kara kasafin kudi ga hukumomin tsaro, domin su samu damar yaki da matsalolin tsaro yadda ya kamata tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin kasa.

A cewarsa, “A wannan rana ta Tunawa da Sojoji, muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan jaruman sojojin da suka rasa rayukansu yayin kare ’yancin kai da mutuncin Nijeriya. Muna kuma kira da a tabbatar da walwala da jin dadin jami’an tsaro domin gudunmuwar da suke bayarwa kada ta zama a banza, tare da rokon Allah Ya ji kan jaruman da suka sadaukar da kansu wajen kare kasa.”

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata