Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaPeter Obi ya yi rajistar shiga jam'iyyar ADC a hukumance

Peter Obi ya yi rajistar shiga jam’iyyar ADC a hukumance

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi ya yi rajista a ADC a ranar Asabar, inda ya jaddada cewa zaɓen 2027 zai kasance tsakanin ‘yan Najeriya da shugabanci mara inganci.

Obi ya ce yankin Kudu maso Gabas na da hakkin samun shugaban kasa, yana mai cewa babu wani yanki da ya fi shi a Najeriya.

Ya kuma jaddada bukatar fitar da ‘yan Najeriya daga talauci don rage rashin tsaro, tare da karfafa masu rajista su yi kokarin jawo sabbin mambobi zuwa ADC.

A wannan rana, Senator Victor Umeh da tsohon dan majalisa Ben Obi ma sun kammala rajista a jam’iyyar a kananan hukumomin Agulu da Awka, Anaocha da Awka South.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata