Ƙasar Rasha ta bayyana aniyarta ta taka rawar shiga tsakani domin sasanta Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da ƙungiyar AES, wadda ta ƙunshi Nijar, Mali da Burkina Faso.
Jakadan Rasha a ƙasashen Bénin da Togo, Igor Evdokimov, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labaran ƙasar Rasha, TASS.
A cewarsa, Moscow na shirin bayar da gudummawa wajen dawo da tattaunawa da fahimta tsakanin ƙasashen ECOWAS da takwarorinsu na ƙungiyar AES, bayan rarrabuwar kawuna da ta ɓulla a baya.
Evdokimov ya ce duk wasu muhimman matakai sun kammala domin buɗe sabbin hanyoyi na ƙarfafa tattaunawa da sulhu tsakanin ɓangarorin biyu.
Kazalika, ya jaddada cewa ƙasar Rasha ta shirya tsaf domin taka rawar shiga tsakanin, a matsayin mai neman samar da fahimta da kwanciyar hankali a yankin Yammacin Afirka.
Rasha na son shiga tsakani don sasanta ECOWAS da ƙungiyar AES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
