Monday, April 6, 2026
HomeKetareRasha na son shiga tsakani don sasanta ECOWAS da ƙungiyar AES

Rasha na son shiga tsakani don sasanta ECOWAS da ƙungiyar AES

Ƙasar Rasha ta bayyana aniyarta ta taka rawar shiga tsakani domin sasanta Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da ƙungiyar AES, wadda ta ƙunshi Nijar, Mali da Burkina Faso.

Jakadan Rasha a ƙasashen Bénin da Togo, Igor Evdokimov, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labaran ƙasar Rasha, TASS.

A cewarsa, Moscow na shirin bayar da gudummawa wajen dawo da tattaunawa da fahimta tsakanin ƙasashen ECOWAS da takwarorinsu na ƙungiyar AES, bayan rarrabuwar kawuna da ta ɓulla a baya.

Evdokimov ya ce duk wasu muhimman matakai sun kammala domin buɗe sabbin hanyoyi na ƙarfafa tattaunawa da sulhu tsakanin ɓangarorin biyu.

Kazalika, ya jaddada cewa ƙasar Rasha ta shirya tsaf domin taka rawar shiga tsakanin, a matsayin mai neman samar da fahimta da kwanciyar hankali a yankin Yammacin Afirka.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata