Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaRikicin PDP na kara yin kamari yayin da bangarorin Damagum da Anyanwu...

Rikicin PDP na kara yin kamari yayin da bangarorin Damagum da Anyanwu ke shirin shiga ofishin jam’iyyar a lokaci guda

Da yiyuwar kara samun rikici a jam’iyyar PDP yayin da bangarorin shugaban jam’iyya Umar Damagum da sakatare Samuel Anyanwu ke shirin komawa aiki a ofishin jam’iyyar na kasa da ke Wadata Plaza, Abuja, a yau Litinin.

A ranar Asabar, bangaren Damagum ya gudanar da taro a Legacy House da ke Maitama, yayin da bangaren Anyanwu kuma ya yi nasa taron a ofishinsa da ke Wuye a Abuja.

Wata majiya daga jam’iyyar ta shaida wa Daily Trust cewa duka bangarorin biyu na shirin yin aiki a ofishin jam’iyyar guda, abin da ke haifar da fargaba a tsakanin ma’aikata na jam’iyyar.

Majiyar ta kara da cewa bangaren Nyesom Wike na kokarin jan hankalin wasu mambobin kwamitin gudanarwa domin samun rinjaye a cikin jam’iyyar, lamarin da zai iya haddasa sabon rikici idan duka bangarorin suka hadu a ofishin a yau.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata