Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiRikicin PDP ya lafa yanzu, amma akwai sauran gyara, Inji Nyesom Wike

Rikicin PDP ya lafa yanzu, amma akwai sauran gyara, Inji Nyesom Wike

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya bayyana cewa rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar adawa ta PDP yanzu ya lafa, sakamakon ficewar wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar.

Wike ya bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa da manema labarai a birnin Abuja a ranar Litinin, inda ya tofa albarkacin bakinsa kan ficewar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar daga jam’iyyar.

Sai dai Wike ya ce duk da cewa an samu sauƙi, har yanzu akwai wasu muhimman matsaloli da ya kamata jam’iyyar ta warware domin samun dawwamammen zaman lafiya.

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas ya kuma bayyana wasu sharudda da, in aka cika su, za su taimaka wajen dawo da cikakken zaman lafiya a jam’iyyar, ciki har da buƙatar tabbatar da sahihancin zaɓen shugabancin jam’iyyar na yankin Kudu maso Kudu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata