Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiRundunar Civil Defence ta Jihar Kano ta cire Kwamandanta na Fagge bayan...

Rundunar Civil Defence ta Jihar Kano ta cire Kwamandanta na Fagge bayan mutuwar wanda ake tsare da shi a ofishin

Hukumar tsaro ta Civil Defence a jihar Kano ta sanar da cire Kwamandan ofishin Fagge bayan mutuwar wani mutum da ake tsare da shi a ofishin. Hukumar ta ce an mika jami’in da aka cire tare da dukkan jami’an da ke bakin aiki a lokacin faruwar lamarin ga rundunar ‘yan sanda domin gudanar da bincike.

Mai magana da yawun NSCDC a Kano, Ibrahim Abdullahi, ya ce Kwamandan jihar, Mohammed Hassan Agalama, ya amince da cire SC Amina Musa Kolawale daga mukaminta, tare da nada CSC Bashir Isa Abubakar a matsayin sabon Kwamandan Fagge.

NSCDC ta bukaci jama’a su kwantar da hankalinsu, tana mai jaddada kudirinta na kare mutuncin rayuwa, hakkin dan Adam da bin doka da ka’idojin aiki, yayin da bincike ke ci gaba kan mutuwar wanda aka tsare.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata