Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiRundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman

Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba.

Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar Kingsley Uwa wanda ya jagoranci sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu a karamar hukumar Gassol da ke jihar, ya nuna illolin da ke tattare da daukar doka a hannu ga jama’a.

Masu ruwa da tsaki da suka hadar da sarakunan gargajiya da sauran jagororin al’umma, sun halarci zaman sulhu da ya gudana a shalkwatar rundunar da ke Jalingo babban birnin jihar.

Wata sanarwa da sashen yada labarai na rundunar ya fitar, ta bayyana cewa akwai bukatar samun hadin kai daga dukkanin bangarori don ganin bayan matsalolin tsaro da ke addabar al’umma.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata