Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiRundunar sojin Njieriya ta jinkirta ritayar wasu dakarunta

Rundunar sojin Njieriya ta jinkirta ritayar wasu dakarunta

Rundunar ta ce hakan ya fito ne sakamakon taɓarɓarewar tsaro da har ta kai ga Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a ƙasar.

An bayyana cewa fiye da mutane 600 aka yi garkuwa da su a watan Nuwamba kaɗai, ciki har da ɗalibai sama da 300 a Jihar Neja, masu ibada 38 a Kwara, da ɗalibai 25 a Kebbi.

Bayan haka ne Shugaba Tinubu ya umarci ƙara yawan jami’an tsaro da kuma tura karin ma’aikata zuwa jihohi.

A cikin wata takarda ta ciki, mai ɗauke da sa hannun Manjo Janar E. I. Okoro a ranar 3 ga Disamba, rundunar ta ce dakatar da ritaya na nufin karfafa aiki yayin da ake faɗaɗa yawan sojoji domin tunkarar matsalar tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata