Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiRundunar ‘yan sandan jihar Kano za ta karfafa tsaro a iyakokin jihar

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano za ta karfafa tsaro a iyakokin jihar

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya gana da kwamandojin rundunar ‘yan sanda don duba dabarun tsaro da karfafa matakan tabbatar da zaman lafiya a fadin jihar.

Taron, da aka gudanar a ranar Litinin a hedkwatar ‘yan sandan ta jihar Kano, ya hada manyan jami’an sassa daban-daban na ayukka da dabaru da leken asiri kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

CP Bakori ya ce taron ya bai wa rundunar damar nazarin nasarorin da aka samu wajen hana laifuka da aiwatar da doka a jihar, tare da tsara hanyoyin kara karfafa ayyukan tsaro, kuma ya jaddada muhimmancin hada kai da al’umma, inda ya umarci shugabannin ayyukan da su karfafa wayar da kan jama’a a matakai na gida.

Hakazalika, ya ce taron ya mai da hankali musamman kan yanayin tsaro a kan iyakokin Kano, musamman karamar hukumomi Shanono, Tsanyawa da Rogo, inda ya bayyana ci-gaban da ake yi wajen kara jami’ai da kayan aiki, tare da bukatar a ci gaba da lura da sabbin barazanar tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata