Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSace dalibai na barazana ga makomarsu a Arewacin Nijeriya - Amnesty International

Sace dalibai na barazana ga makomarsu a Arewacin Nijeriya – Amnesty International

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International a Nigeria ta yi gargadin cewa yawaitar sace dalibai a makarantun arewa na iya karya ilimi, tare da jefa rayuwar yara cikin mummunar makoma.

A wata hirar da ya yi a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin, daraktan Amnesty a Nijeriya Isa Sanusi ya ce tsananin tsoro da fargabar sace dalibai na hana su zuwa makaranta, lamarin da ke kara dagula fannin ilimi a yankin.

Sanusi ya bayyana cewa iyayen da ke fama da talauci musamman a karkara na fama wajen tura yaransu makaranta, a yayin da rashin tsaro da sace-sacen yara zai kara hana su yarda da aika ’ya’yansu makaranta.

Ya ce tsoron sace wa kaɗai zai hana dubban yara samun ilimi a arewacin Nijeriya wanda a yanzu yaran da ba sa zuwa makaranta sun haura miliyan 12.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata