Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaSanata daga jihar Cross River ya sauya sheka daga PDP zuwa APC

Sanata daga jihar Cross River ya sauya sheka daga PDP zuwa APC

Sanata Agom Jarigbe mai wakiltar mazabar Arewa ta jihar Cross River ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, inda ya sanar da majalisar dattawa ta hanyar aika wasiƙa a hukumance.

A yayin zaman majalisar da aka watsa kai tsaye a NASSTV a ranar Talata, mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya Barau Jibrin, ya karanta wasiƙar ficewar sanatan, inda Jarigbe ya ce rikice-rikicen cikin gida a PDP ne suka tilasta masa daukar matakin ficewar.

Jarigbe ya bayyana cewa ya yanke wannan shawara ne bayan tunani mai zurfi kan halin da jam’iyyar ta tsinci kanta a matakin jiha da kasa, inda ya koka da rarrabuwar kawuna da rashin sulhu a cikinta.

A cewarsa, jam’iyyar APC ce ke ba shi cikakken dandali na ci-gaba da gudanar da ayyukan da za su amfani al’ummar mazabarsa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata