Sarkin Daura, Alhaji Faruq Umar Faruq, ya tsige Iliya Mantau, Dagacin Mantau a karamar hukumar Baure, bisa zarginsa da hannu wajen sace wata mata da jaririyarta tare da yi mata fyade.
Tsige shi ya biyo bayan zanga-zangar matasa da korafe-korafen da mazauna garin Yarmaulu suka shigar, inda aka zargi Dagacin da wasu da laifin garkuwa da Zulaihatu da karbar kudin fansa N20m kafin yi mata lalata.
Lamarin da ya jima yana gaban kotu, ya janyo ce-ce-ku-ce saboda jinkirin daukar mataki daga masarauta na tsawon kusan shekara guda.
