Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSarkin Musulmi ya bukaci gwamnoni da su rika sauraron masu sukarsu

Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnoni da su rika sauraron masu sukarsu

Sarkin ya bayyana haka ne a taron Gwamnonin Arewa da majalisar sarakunan gargajiya da aka gudanar a Kaduna a Litinin din nan, Sarkin Musulmi ya ce babu wani shugaban da zai nemi kuri’ar jama’a sannan ya yi watsi da su bayan hawa mulki.

Ya kuma bayyana damuwarsa kan yadda ake yawan zargin gwamnonin da rashin daukar mataki, ya jaddada cewa kamata ya yi su fuskanci abubuwanda ke gabansu, musamman wajen yakar rashin tsaro, talauci da matsalolin tattalin arziki.

A cewarsa, ya zama wajibi shugabanni su dinga sauraron sukar da ake musu cikin lumana domin hakan na iya jagorantar su wajen yin abinda ya kamata ga al’ummarsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata