Babbar Kotun Ƙolin Saudiyya ta bukaci dukkan Musulmi a faɗin Masarautar su fara duban jinjirin watan Ramadan a yammacin ranar Talata, 29 ga Sha’aban 1447AH, wanda ya yi daidai da 17 ga Fabrairu, 2026.
Kamar yadda Majalisar ta bayyana a sanarwar da shafin Haramain ya fitar, duk wanda ya hango jinjirin da idon sa ko ta na’urar hangen nesa, ya garzaya kotun da ta fi kusa da shi domin ba da shaidarsa.
