Monday, April 6, 2026
HomeKetareSaudiyya za ta gina rijiyoyin butsatse 78 a Nijeriya

Saudiyya za ta gina rijiyoyin butsatse 78 a Nijeriya

Cibiyar bayar da agaji ta Sarki Salman na kasar Saudiyya (KSrelief) ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa da wata kungiya don gina rijiyoyin burtsatse 78 masu amfani da hasken rana a jihohi 10 Nijeriya.

Wata sanarwar ta ce ana sa ran shirin zai samar da ruwan sha ga kusan mutane 733,350, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Mataimakin babban mai kula da ayyuka da shirye-shirye na Cibiyar KSrelief, Engr Ahmed bin Ali Al-Baiz ya sanya hannu kan yarjejeniyar a hedkwatar KSrelief da ke birnin Riyadh.

Ta ce yarjejeniyar tana da nufin samar da tsaftataccen ruwan sha ga mutane da dabbobi, da kuma inganta samar da tsaftatattun ruwan sha a yankunan karkara.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata