Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSaurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa hakora shida.

Lamarin ya faru ne ranar Asabar, 12 ga Yuli, 2025, bayan wata gajeriyar cacar baki tsakanin masoyan da ta rikide zuwa tashin hankali.

Rahotanni sun nuna cewa Fatima ta kwanta a asibiti sakamakon munin dukan da saurayin nata ya yi mata, lamarin da ya jawo fargaba da kuka daga iyalanta, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata