Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare da dawo da amincewa ga ƙasar.
Shettima ya bayyana hakan ne a taron yaye wadanda aka horas kan sana’o’i da aka gudanar a State House Conference Hall, Abuja.
Mataimakin shugaban ƙasar, wanda Sanata Ibrahim Hadejia ya wakilta, ya ce halartar ƙwararru daga ƙasashen waje a shirye-shiryen mika takardun kammala samun horon na nuna ƙara amincewa da Nijeriya a duniya.
Ya ce yaye ƙwararru 2,100 karon farko a fannin sayen kayayyaki (procurement) daga Nijeriya da wasu ƙasashe alama ce ta jajircewar gwamnatin Tinubu wajen aiwatar da Renewed Hope Agenda.
