Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiSERAP ta maka Akpabio da Abbas kotu bisa zargi kasa bayyana...

SERAP ta maka Akpabio da Abbas kotu bisa zargi kasa bayyana yadda aka kashe Naira biliyan 18 na kudin majalisa

Kungiyar SERAP ta shigar da ƙara a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja kan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, bisa zargin rashin bayyana yadda aka kashe ₦18.6bn da aka ware domin ginin ofishin hukumar kula da ayyukan majalisa (NASC).

SERAP ta shigar da ƙarar ne a makon da ya gabata, inda aka ambaci Akpabio da Abbas a madadin dukkan ’yan majalisar, tare da sanya NASC a matsayin mai amsa ƙara.

A cewar sanarwar da mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya fitar ranar Lahadi, ƙarar ta biyo bayan munanan zarge-zarge da ke cikin rahoton mai duba asusun kuɗi na tarayya na 2022, wanda aka wallafa a 9 ga watan Satumba 2025.

SERAP ta ce rahoton ya nuna NASC ta biya fiye da ₦11.6bn ga wani kamfani da ba a bayyana ba domin ginin sabon ofishinta cikin watanni 24, inda kuma aka ce an ƙawata kwangilar da fiye da ₦6.9bn a wani canji da aka yi ba tare da tsarin daukar kwangila ba.

Kungiyar ta kara da cewa an bayar da kwangilolin ne ba tare da tantance bukata, tallar jarida, yin gasa, kwangila ta rubuce ko amincewar Majalisar Zartaswa ta Tarayya, haka kuma babu takardar ‘No Objection’ daga Hukumar BPP.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata