Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSERAP ta maka Akpabio da Abbas kotu kan zargin cin hanci na...

SERAP ta maka Akpabio da Abbas kotu kan zargin cin hanci na Naira miliyan 3 a majalisar dokoki

Kungiyar SERAP ta shigar da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, kotu saboda kin bincikar zargin cewa ‘yan majalisa suna biyan har Naira miliyan uku domin gabatar da kudiri ko koke a majalisar.

Karar ta biyo bayan wani faifan bidiyo da dan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Ibrahim Auyo, ya yada inda ya ce ana karɓar tsakanin Naira miliyan 1 zuwa 3 domin a gabatar da kudiri ko koke a majalisar.

SERAP ta nemi kotu ta tilasta wa Akpabio da Abbas su mika lamarin ga hukumomin yaki da cin hanci don bincike da gurfanarwa, tare da daukar matakan kare Ibrahim Auyo da ya fallasa zargin.

Kungiyar ta ce wannan zargi babban cin amanar jama’a ne da ya sabawa rantsuwar kama aiki, tana mai jaddada cewa bai kamata cin hanci ya zama sharadi wajen gudanar da ayyukan majalisa ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata