Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiSERAP ta soki gwamnatin Tinubu game da karin fasfo

SERAP ta soki gwamnatin Tinubu game da karin fasfo

Ƙungiyar SERAP mai fafutikar tabbatar da adalci da shugabanci nagari ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta soke ƙarin kuɗin fasfo da hukumar shige da fice ta sanar, wanda tace anyi ba bisa ka’ida ba.

A cewar sanarwar da mataimakin daraktan kungiyar, Kolawole Oluwadare, ya sanya wa hannu, wannan sabon ƙarin kuɗin zai toshe wa miliyoyin talakawa damar samun fasfo mai shafuka 34 na shekaru 5 da mai shafuka 64 na shekaru 10.

Wannan ne karo na uku cikin shekaru biyu da ake yin ƙarin kuɗaɗen fasfo, kuma zai fara aiki a watan Satumba 2025 kafin.

A bara, cikin watan Agusta 2024 aka yi irin wannan karin kudin fasfon a Nijeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata