Tuesday, April 7, 2026
HomeKetareShugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe...

Shugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe a Kamaru

Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da dadadden tarihi tsakanin kasashen biyu.

A cewar rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar China ta wallafa a ranar Juma’a, Xi ya bayyana cewa kasashen biyu sun gina amincewar juna ta siyasa tare da cimma manyan nasarori a fannonin hadin gwiwa daban-daban a cikin ‘yan shekarun nan.

Xi ya kara da cewa kasar China za ta cigaba da inganta huldar diflomasiyya, tattalin arziki da al’adu da kasar Kamaru a kokarin da take yi na karfafa alaka da nahiyar Afirka.

Haka kuma, ya jaddada cewa kasashen biyu suna ci-gaba da marawa juna baya kan muhimman al’amura da bukatun da suka shafi kasashensu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata