Shugaba Bola Tinubu ya ya aike da tsohon ministan cikin gida, Abdulrahman Dambazau, wanda ya taba zama shugaban sojin ƙasa, a matsayin jakada domin tantancewa a majalisa.
Haka kuma a cikin sunayen akwai Ibok-Ete Ekwe Ibas, tsohon kwamandan sojin ruwa kuma tsohon shugaban rikon Rivers.
Sauran sun hada da Ita Enang, tsohon sanata, da Chioma Ohakim, tsohuwar uwargidan jihar Imo.
Wannan na zama rukuni na uku na jerin jakadu da shugaban ya aika majalisa domin tantancewa.
Fadar shugaban kasa ta ce sabon jerin sunaye na kunshe ne da mutane da za su wakilci ƙasar a muhimman ƙasashe, domin karfafa dangantaka da kare muradin Nijeriya a ketare.
