Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 712.3 domin gudanar da cikakken gyaran filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Lagos, a wani bangare na kokarin farfado da bangaren sufurin jiragen sama a karkashin shirin Renewed Hope Infrastructure Development Fund.
Ministan sufurin jiragen sama Festus Keyamo, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Kasa jim kadan bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Abuja ranar Alhamis.
Keyamo ya bayyana cewa wannan ne karo na farko da za a gudanar da cikakken gyaran tsohon ginin filin jirgin tun daga lokacin da aka gina sa.
A cewarsa, za a kammala aikin cikin watanni 24, kuma yana daga cikin shirin sabunta muhimman ababen more rayuwa da suka hada da sabunta filin saukar jirage da fitilun sauka a Port Harcourt da za a kashe Naira biliyan 42.1bn, da jiha Kano da za a kashe Naira biliyan 46.3bn, sai Lagos da aka ware Naira biliyan 44.1bn, domin rage jinkirin saukar jirage da ke faruwa sakamakon yanayi mara kyau.
Shugaba Tinubu ya amince da kashe Naira biliyan 712.3 don gyaran filin jirgin saman Lagos
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
