Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya bukaci Sojojin Nijeriya da su kasance masu biyayya ga...

Shugaba Tinubu ya bukaci Sojojin Nijeriya da su kasance masu biyayya ga dimokradiyya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bukaci dakarun sojin Nijeriya su cigaba da kasancewa masu ladabi, biyayya da haɗin kai, yana mai bayyana su a matsayin alamar ƙarfin bai ɗaya da kuma masu kare dimokuraɗiyyar ƙasa. Shugaban ya bayyana hakan ne ta bakin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, a bikin Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026 (AFCRD).

Tinubu ya ce walwalar sojoji ba ta rabu da tsaron ƙasa ba, inda ya ba su tabbacin ingantattun kayan aiki, horaswa da kyakkyawan yanayin rayuwa, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta cigaba da tallafa musu domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin ƙasar.

Shugaban ya kuma jinjinawa jaruman da suka rasu wajen kare Nijeriya, yana cewa tunawa da su hakki ne na ƙasa baki ɗaya, ba wai biki kawai ba. Haka kuma, ya sanar da ƙaddamar da shirye-shirye guda biyu, Thank-A-Soldier Electronic Wall da My Nigerian Hero Campaign domin bai wa ’yan Nijeriya damar girmama sojoji da tsoffin dakarun ƙasa, yayin da aka karrama wasu manyan jami’an soja masu aiki da masu ritaya a taron.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata