Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya jaddada aniyar gwamnatin tarayya wajen inganta horo da walwar...

Shugaba Tinubu ya jaddada aniyar gwamnatin tarayya wajen inganta horo da walwar jami’an tsaro

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar da goyon bayan gwamnati ga ‘yan sanda ta hanyar ingantaccen horo, kayan aiki, da jin dadin ma’aikata, tare da magance tushen rashin tsaro ta ci-gaban tattalin arziki, a yayin bikin kammala horon sabbin ‘yan sanda 1,001 a makarantar horon ‘yan sanda da ke a Wudil, Kano.

Sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, ya ce sabbin jami’an suna da alhakin girmama hakkin bil’adama, gudanar da aiki cikin gaskiya, da kare doka yayin da suke shiga aiki a fagen tsaron cikin gida.

Kwamandan POLAC, AIG Patrick Atayero, ya bayyana cewa ‘yan sandan da aka yaye din sun sami cikakken horo na ilimi da aikin aiki, kuma cibiya na ci-gaba da fadada shirye-shirye da inganta gine-gine domin daidaita aikin ‘yan sanda da matakan kasa da kasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata