Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya ja kunnen gwamnoni da su inganta rayuwar talakawa

Shugaba Tinubu ya ja kunnen gwamnoni da su inganta rayuwar talakawa

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bukaci gwamnonin jihohi da su kara mayar da hankali wajen inganta rayuwar al’ummar karkara ta hanyar zuba jari a bangarorin da suka shafi kawar da talauci, inganta lantarki, bunkasa noma da gina ababen more rayuwa.

Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin taron majalisar tattalin arzikin kasa (NEC) karo na 150 da aka gudanar a fadar shugaban kasa a Abuja, inda ya ce dole ne gwamnoni su hada kai da gwamnatin tarayya domin farfado da tattalin arzikin yankunan karkara.

Ya kuma bukaci a rungumi amfani da injuna a harkokin noma, a yaki matsalar rashin tsaro, sannan a kara shigar da yara makaranta ta hanyar ci gaban shirin ciyar da dalibai a makarantu.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman kan harkar yaɗa labarai a ofishin mataimakin shugaban kasa, Stanley Nkwocha ya fitar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata