Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, murnar cika shekaru 76 a ranar 25 ga Disamba.
Tinubu ya bayyana Dr. Ganduje a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren mai gudanarwa, wanda ya yi wa ƙasa hidima a mukamai daban-daban tsawon kusan shekaru 50, ciki har da zama mataimakin gwamna da gwamnan Jihar Kano na wa’adi biyu.
Hakazalika, ya ce yana matuƙar godiya ga zumunci da haɗin gwiwar da ke tsakaninsa da Ganduje, yana mai addu’ar Allah Ya ƙara masa lafiya da tsawon rai domin ci-gaba da yi wa Nijeriya da al’umma hidima.
