Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya umarci a sauke tutar Nijeriya zuwa rabin sanda a...

Shugaba Tinubu ya umarci a sauke tutar Nijeriya zuwa rabin sanda a fadin kasar domin jimamin rasuwar Buhari

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu yau Lahadi a birnin London da misalin ƙarfe 4:30 na yamma bayan doguwar jinya.

Shugaba Tinubu ya sha mika ta’aziyyarsa ga uwargidan marigayin, Hajiya Aisha Buhari, tare da umartar mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, da ya tafi Birtaniya domin dawo da gawar shugaban zuwa gida Najeriya.

Buhari ya shugabanci Najeriya a matsayin shugaban ƙasa na mulkin farar hula daga 2015 zuwa 2023, kuma ya rike kujerar shugaban ƙasa a lokacin mulkin soja daga shekarar 1984 zuwa 1985.

A wani mataki na girmamawa, Shugaba Tinubu ya umarci a sauke tutar Najeriya zuwa rabin sanda a fadin kasar, a matsayin alamar alhini da karramawa ga rayuwar marigayin shugaban ƙasa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata