Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja,...

Shugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja, Kano da Rivers

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a, jami’an tsaro da jami’an Hukumar zaɓe Mai zaman kanta (INEC) da su gudanar da ayyukansu cikin tsari da natsuwa yayin zaɓukan da za a yi ranar Asabar a Babban Birnin Tarayya (FCT), Kano da Rivers.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa Shugaban kasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, shugaban ya bukaci duk masu haƙƙin zaɓe su fito su kaɗa ƙuri’a ba tare da tsoro ba.

INEC za ta gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomi shida na FCT, da kuma zaɓukan cike gurbi a mazabun Ahoada East II da Khana II a Jihar Rivers, da Kano Municipal da Ungogo a Jihar Kano.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata