Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa zai gana da shugaban kasar Amurka Donald Trump a fadar White House a dai-dai lokacin da ake ci gaba da samun takun-saka tsakanin kasashen biyu.
Ana sa ran za a tattauna muhimman batutuwan da suka hada da dokar sake fasalin kasa a Afirka ta Kudu, rikicin Isra’ila da Gaza, harajin shigo da kaya Amurka.
Ramaphosa na da nufin kare manufofin kasashen waje na Afirka da yin shawarwari kan sabunta dokar ci gaban Afirka da dama wacce ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Afirka.
