Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiShugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da...

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar da ta sake yin nasara.

Wannan mataki ya biyo bayan zarge-zargen magudi da gallazawa daga gwamnati da ‘yan adawa suka yi, lamarin da ya haddasa zanga-zanga mai muni tare da rasa rayukan daruruwan mutane.

Kungiyoyin kare hakkin dan adam da ‘yan adawa sun ce an halaka mutanen ne a lokacin da aka katse intanet baki ɗaya a kasar.

A jawabinta na farko a gaban majalisar bayan sake zabenta, Shugaba Samia ta umarci ‘yan sandan kasar da jami’an tsaro su sassauta wa matasa masu zanga-zanga.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata