Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiSojoji a Guinea-Bissau sun rantsar da sabon shugaban rikon kwarya

Sojoji a Guinea-Bissau sun rantsar da sabon shugaban rikon kwarya

A ranar Alhamis, rundunar sojin Guinea-Bissau ta sanar da cewa an rantsar da Janar Horta Nta Na Man a matsayin sabon shugaban rikon kwarya, kwana guda bayan da suka hambarar da gwamnatin kasar.

A cewar sanarwar da sojin ƙasar suka fitar, rantsuwar ta biyo bayan jawabin da hafsoshin rundunar suka yi tun a ranar Laraba inda suka bayyana cewa sun kifar da shugaban ƙasar da ke kan mulki.

Rahotanni daga France24 sun bayyana cewa wannan matakin ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara samun tashe-tashen hankula a yankin Yammacin Afirka, musamman game da karuwar juyin mulki a wasu kasashe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata