Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSojoji sun dakile yunkurin garkuwa da 'yan bautar kasa

Sojoji sun dakile yunkurin garkuwa da ‘yan bautar kasa

Dakarun haɗin gwiwa na “Operation Hadin Kai” sun dakile wani yunkurin garkuwa da masu yi wa kasa hidima 74 a hanyar Buratai zuwa Kamuya, jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar, Manjo Sani Uba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Alhamis, inda ya ce sojojin sun yi gaggawar kai dauki bayan motocin ɗaliban sun lalace a wurin da ake yawan yin garkuwa da mutane.

A cewar sa, masu yi wa kasa hidimar maza 36 da mata 38, motar tasu ta lalace ne da misalin ƙarfe 9:05 na dare a ranar Talata.

Sojojin sun gano matasan suna cikin haɗari, suka garzaya suka kwashe su zuwa sansanin soja da ke Buratai don kare su daga yiwuwar hare-haren ‘yan ta’addan.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata