Dakarun rundunar sojin Najeriya ta 12 Brigade, karkashin Operation Accord III, tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, sun yi nasarar halaka wani kwamandan ‘yan bindiga mai suna Babangida Kachala, wanda shi ne mataimakin shugaban dabar da Kachala Shuaibu ke jagoranta a dajin Masalaci Boka da Ofere, Jihar Kogi.
Wannan nasarar ta zo ne mako guda kacal bayan da sojoji suka yi nasarar kashe wani babban kwamandan dabar, Kachalla Balla, tare da wasu ƴan bindiga biyar.
Haka kuma, dakarun tare da tallafin jiragen sama sun gudanar da wasu hare-haren share fagen da ya kai ga ceto fursunonin da aka sace.
Mai magana da yawun rundunar, Lieutenant Hassan Abdullahi, wanda shi ne mukaddashin daraktan hulɗa da jama’a na 12 Brigade, ya tabbatar da wannan nasara a cikin wata sanarwa da aka fitar daga Lokoja a ranar Asabar.
Sojoji sun hallaka wani kwamandan ‘yan bindiga a jihar Kogi
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
